• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu

by Bello Hamza
11 months ago
in Tattalin Arziki
0
Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu Nijeriya da kasar Amurka sun jaddada shirin kara karfafa harkokin kasuwanci da zuba jari a tsakaninsu.

 

Wannann ya biyo bayan taron koli nena kasashen da ya gudana a tsakanin Ministar Masa’anatu, Kasuwanci da Zuba Jari na Nijeriya, Dakta Doris Uzoka-Anite, da tawagar kasar Amurka a karkashin jagorancin mataimakin sakatare mai kula da harkokin ciniki da kasuwanci tsakanin kasashen waje, Mista Arun Benkataraman, a Abuja ranar Laraba.

  • Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Na Shirin Shiriricewa
  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa

Taron ya mayar da hankali ne wajen karfafawa tare da tabbatar da yarjejeniyar da ke tsakanin kasashen biyu da suka hada da shirin nan na (TIFA) da (AGOA) da (BNC) da kuma (CID) wadanda ke karfafa kasuwanci a tsakanin kasashen Afrika da duniya baki daya ba a manta da su ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Duka bangarorin sun karfafa bukatar fadada harkokin kasuwanci a tsakaninsu tare da kuma kirkiro da sabbin hanyoyin cimma bukatun kasashen nasu domin bunkasa tattalin arzikin juna.

 

Dakta Uzoka-Anite ta bayyana abubuwan da Amurka za ta amfana dasu a Nijeriya wadanda suka hada da kasancewar ta babbar kasuwar da babu irinta a nan kusa da kuma ma’adanai da Allah ya hore mana a sassan kasa, haka kuma muna da kwararru masu ilimi daban-daban da za a iya fitar dasu zuwa kasashen waje su amfanar da kasashe daban-daban,” in ji ta.

 

Ta kuma jinjina wa dangantakar da ke tsakanin Nijeriya da Amurka. “Nijeriya da Amurka sun dade suna hulda da juna na tsawon shekaru, suna mutunta juna tare da amfanar juna a bangarorin tattalin arziki da dama,” in ji ta.

 

A nasa jawabin, Benkataraman ya sanar da goyon bayan Amurka ga shirin farfado da tattalin arzikn kasa da kuma irin kalubalen da kamfanonin Amurka da ke harkoki a Nijeriya ke fuskanta.

 

“Za mu yi aiki domin karfafa dangantakar da ke tsakanin mu domin samun ci gaba da bunkasar tattalin arziki ta yadda al’ummar kasashen biyu za su amfana,” in ji shi.

 

Tawagar ta kasa Amurka ta nuna sha’awarta ga sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu take yi, sun kuma yi alkawarin bayar da gudummawarsu wajen karfafa kasuwanci da zuba jari a Nijeriya a daidai wannan lokacin.

 

Duka bangarorin sun amince da ci gaba da tattaunawa akai akai tsakaninsu don tabbatar da dorewar yarjejeniyar da aka kulla. An kammala taron tare da alkawarin kara karfafa kasuwanci da zuba jari a tsakanin kasashen biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Afirka da AmurkaBunkasa Tattalin ArzikiGwamnatin Tarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

Related

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 week ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
Next Post
BUK

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.