• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Masu Bayyana Ra’ayi Sun Zargi USADA Da Yin Rufa-rufa

by Sulaiman and CGTN Hausa
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Masu Bayyana Ra’ayi Sun Zargi USADA Da Yin Rufa-rufa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Batun rufa-rufa game da dan wasan tseren Amurka Erriyon Knighton da aka zarga da amfani da abubuwa masu kara kuzari yayin wasa, ya bankado zargin da ake yiwa hukumar yaki da amfani da abubuwan kara kuzari yayin wasanni ta Amurka wato USADA da boye gaskiya, da yin fuska biyu, da amfani da karfin iko ba bisa ka’ida ba.

Game da hakan, wasu kuri’un al’umma da kafar CGTN ta tattara sun nuna kaso 95.57 bisa dari na al’ummun da suka bayyana ra’ayoyinsu daga sassa daban daban na duniya, na zargin USADA da yiwuwar rufe gaskiya kan ’yan wasan Amurka, da aka tabbatar sun yi amfani da abubuwa masu kara kuzari.

  • Hukumar Yaki Da Shan Maganin Kara Kuzari Yayin Wasanni Ta Duniya Ta Fallasa Ayyukan Amurka Game Da ’Yan Wasa Masu Keta Ka’idoji
  • Ya Kamata Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Karshen Matsin Rayuwa – Gwamnan Bauchi 

A watan Maris da ya shude, hukumar yaki da amfani da abubuwa masu kara kuzari yayin wasanni ta kasa da kasa WADA, ta samu Erriyon Knighton da laifin amfani da abubuwan kara kuzari, amma duk da haka hukumar USADA ta kyale shi ya shiga wasu wasanni ba tare da la’akari da hukuncin WADA ba. Sai dai kawai USADA ta ce wai dan wasan ya ci wani nama ne gurbataccen wanda ya sanya aka same shi da wancan laifi.

Amma a daya bangaren WADA ta fitar da sanarwa, inda ta ce ba ta taba baiwa hukumar USADA ikon barin irin wadannan ’yan wasa da aka kama da lafin su shiga gasanni ba, domin hakan zai iya zubar da kimar gasanni.

Game da hakan, sakamakon kuri’un jin ra’ayi na CGTN, sun nuna cewa kaso 90.15 na jama’ar da suka bayyana matsayar su na ganin Amurka ta rufe laifin Knighton, har ta ba shi damar shiga gasar Olympic ta birnin Paris, wanda hakan ya yi matukar gurgunta kima da makasudin gasanni. Har ila yau, kaso 96.54 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na ganin abun da Amurka ta yi misali ne na yin fuska biyu. Yayin da wani kason da ya kai 95.63 bisa dari ke ganin da yawa daga yan wasan Amurka na gabatar da shaidun bogi na gwaje gwajen da aka yi musu.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Bugu da kari akwai kaso mai yawa da ya kai 96.23 bisa dari dake ganin ya dace a kara yawan gwajin da ake yiwa ’yan wasan Amurka masu halartar gasar Olympic ta Paris, domin dawo da kima da kwarin gwiwar adalci tsakanin sassan kasa da kasa kan gasar.

An gudanar da kuri’un jin ra’ayin al’ummar na CGTN ne ta harsunan Turanci da Faransanci, da Larabci, da harsunan Sifaniya da Rasha, inda masu bayyana ra’ayi 14,580 suka fayyace matsayarsu cikin sa’o’i 16.
(Mai Fassara: Saminu Alhassan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dole Ne Bangaren Amurka Ya Mai Da Martani Ga Duniya Game Da Amfani Da Maganin Kara Kuzari Yayin Wasanni

Next Post

Kasar Sin Ta Yi Karar EU A WTO Kan Matakan Wucin Gadi Kan Motocin Lantarki Na Kasar Sin

Related

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam
Daga Birnin Sin

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

12 hours ago
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

13 hours ago
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

14 hours ago
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

15 hours ago
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

16 hours ago
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

17 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Karar EU A WTO Kan Matakan Wucin Gadi Kan Motocin Lantarki Na Kasar Sin

Kasar Sin Ta Yi Karar EU A WTO Kan Matakan Wucin Gadi Kan Motocin Lantarki Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.