ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Masu Bayyana Ra’ayi Sun Zargi USADA Da Yin Rufa-rufa

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Cgtn

Batun rufa-rufa game da dan wasan tseren Amurka Erriyon Knighton da aka zarga da amfani da abubuwa masu kara kuzari yayin wasa, ya bankado zargin da ake yiwa hukumar yaki da amfani da abubuwan kara kuzari yayin wasanni ta Amurka wato USADA da boye gaskiya, da yin fuska biyu, da amfani da karfin iko ba bisa ka’ida ba.

Game da hakan, wasu kuri’un al’umma da kafar CGTN ta tattara sun nuna kaso 95.57 bisa dari na al’ummun da suka bayyana ra’ayoyinsu daga sassa daban daban na duniya, na zargin USADA da yiwuwar rufe gaskiya kan ’yan wasan Amurka, da aka tabbatar sun yi amfani da abubuwa masu kara kuzari.

  • Hukumar Yaki Da Shan Maganin Kara Kuzari Yayin Wasanni Ta Duniya Ta Fallasa Ayyukan Amurka Game Da ’Yan Wasa Masu Keta Ka’idoji
  • Ya Kamata Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Karshen Matsin Rayuwa – Gwamnan Bauchi 

A watan Maris da ya shude, hukumar yaki da amfani da abubuwa masu kara kuzari yayin wasanni ta kasa da kasa WADA, ta samu Erriyon Knighton da laifin amfani da abubuwan kara kuzari, amma duk da haka hukumar USADA ta kyale shi ya shiga wasu wasanni ba tare da la’akari da hukuncin WADA ba. Sai dai kawai USADA ta ce wai dan wasan ya ci wani nama ne gurbataccen wanda ya sanya aka same shi da wancan laifi.

ADVERTISEMENT

Amma a daya bangaren WADA ta fitar da sanarwa, inda ta ce ba ta taba baiwa hukumar USADA ikon barin irin wadannan ’yan wasa da aka kama da lafin su shiga gasanni ba, domin hakan zai iya zubar da kimar gasanni.

Game da hakan, sakamakon kuri’un jin ra’ayi na CGTN, sun nuna cewa kaso 90.15 na jama’ar da suka bayyana matsayar su na ganin Amurka ta rufe laifin Knighton, har ta ba shi damar shiga gasar Olympic ta birnin Paris, wanda hakan ya yi matukar gurgunta kima da makasudin gasanni. Har ila yau, kaso 96.54 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na ganin abun da Amurka ta yi misali ne na yin fuska biyu. Yayin da wani kason da ya kai 95.63 bisa dari ke ganin da yawa daga yan wasan Amurka na gabatar da shaidun bogi na gwaje gwajen da aka yi musu.

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Bugu da kari akwai kaso mai yawa da ya kai 96.23 bisa dari dake ganin ya dace a kara yawan gwajin da ake yiwa ’yan wasan Amurka masu halartar gasar Olympic ta Paris, domin dawo da kima da kwarin gwiwar adalci tsakanin sassan kasa da kasa kan gasar.

An gudanar da kuri’un jin ra’ayin al’ummar na CGTN ne ta harsunan Turanci da Faransanci, da Larabci, da harsunan Sifaniya da Rasha, inda masu bayyana ra’ayi 14,580 suka fayyace matsayarsu cikin sa’o’i 16.
(Mai Fassara: Saminu Alhassan)

 

Cgtn
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
  • Sulaiman
    Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
Cgtn
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Karar EU A WTO Kan Matakan Wucin Gadi Kan Motocin Lantarki Na Kasar Sin

Kasar Sin Ta Yi Karar EU A WTO Kan Matakan Wucin Gadi Kan Motocin Lantarki Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Cgtn

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Cgtn

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.