• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Shayar Da Jarirai Da Sauran Sauye-sauyen Da Aka Samu A Gasar Olympics

by Abba Ibrahim Wada
12 months ago
in Wasanni
0
Tsarin Shayar Da Jarirai Da Sauran Sauye-sauyen Da Aka Samu A Gasar Olympics
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ake ci gaba da gudanar da wasannin guje-guje da tsalle-tsalle na duniya Olympic, abubuwa da dama suna faruwa a gasar ciki har da batun mata masu shayarwa da masu ciki da suka tsinci kansu a ci-kin gasar ta wannan shekarar.

Lokacin da ‘yar tseren yada-kanin-wani Aliphine Tuliamuk ta tashi zuwa gasar Olympics ta Tokyo a 2021, abu daya da yake a zahiri shi ne cewa ba za ta je sansanin gasar da ‘yarta ‘yar wata shida ba, mai suna Zoe.

  • Muna Samun Nasarori A Yaki Da Gurbatattun Masana’antar Kannywood – Tijjani Asase
  • Sin Ta Ki Amincewa Da Duk Wanda Ya Yi Amfani Da Gasar Olympics Wajen Yada Yunkurin ‘Yan Aware Na Yankin Taiwan

A hirarta da manema labarai, ta ce “ Na yi kuka sosai a lokacin da aka dauke mu a motar bas zuwa san-sanin ‘yan wasa. Ba abin da nake yi sai kallon bidiyo da hotunan ‘yata. Da na isa sansanin ba na iya bacci ba tare da ita ba.”

Gasar ta kasance a lokacin da ake tsaka da annobar Korona, kuma gasar da Tuliamuk za ta yi za ta kasance ne a Birnin Sapporo na Arewacin Japan, kuma hakan na nufin Tuliamuk za ta iya kasancewa da iyalinta, sai dai kawai lokacin da ta kasance cikin damuwa shi ne, daren farko da ta kasance a sansanin da ‘yan gasar suka zauna a Tokyo inda aka haramta zuwa da yara.

Wannan ne dalilin da ya sa ‘yar tseren ta Amurka haifaffiyar Kenya ta yi maraba da tsarin da aka bullo da shi na barin mata masu shayarwa da masu kula da jariransu su halarci gasar Paris 2024, ciki har da samar da wani waje na yadda mata za su iya ganawa da jariransu a sansanin.

Labarai Masu Nasaba

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

“Ina matukar farin ciki cewa cikin shekara hudu kawai daga lokacin da ba zan iya kasancewa da jaririyata ba, an samu sauyi inda yanzu za ka iya kasancewa da su. Wannan babban cigaba ne,” a cewarta

Batun lokacin da mace da ke gasar za ta daina shayar da jaririnta na daya daga cikin abubuwan da Tuliamuk, da ire-irenta suka yi fama da shi, hukumar lafiya ta duniya, WHO, ta bayar da shawarar bai wa jariri nonon uwa zalla tsawon wata shida na farko, sannan a ci gaba da shayar da shi hadi da isasshen abinci har zuwa shekara biyu ko sama da haka.

“Zan shayar tsawon wata uku ko hudu, wanda wannan zai ba ni kusan wata biyu da rabi kafin gasar Olympics, to amma ina haihuwa sai na fahimci cewa dakatar da shayarwa ba abu ne da zan iya ba. Abu ne da nake matukar so,” i n ji Tuliamuk.

Wannan na daga cikin abubuwan da suka sa hukumar wasan Olympics ta duniya da masu shirya gasar ta Birnin Paris ta shekarar nan, a karon farko a tarihin Olympic suka samar da waje na musamman na zuwa da yara gasar.

“Mun yi nazari sosai daga abubuwan da suka faru a gasar Tokyo da sauran wadanda aka yi a baya, muka yi tunanin kawo wani sauyi mu inganta gasar” kamar yadda Emma Terho, ta hukumar gasar ta Olympic ta bayyana.

Muna da tarin mata matasa da ke da jarirai kanana, da kuma mata da ke ci gaba da sana’arsu ta wasan bayan sun haihu domin a cewarta sun lura cewa za su fi mayar da hankali sosai a gasar idan akwai wuraren da za su iya ganin jariransu da masu kula da jariran a wajen gasar.

Saboda haka ne aka samar da wani waje na musamman a sansanin gasar, inda mai shayarwa za ta iya samun ganin jaririnta a kebe, ta tatsi nono a ajiye domin bai wa jaririn da dai sau-ran abubuwa na kula da jaririn.

Akwai damar ma da mai shayarwa za ta iya kwana a wajen tare da jaririnta, idan har hukumomin shirya gasar na kasashe suka yarda su samar da kudaden gudanar da su sai dai tsohuwar ‘‘yar gasar Olympic ta huturu, Terho, ta ce akwai tsarin da mai shayarwa da ke matukar bukatar wajen za ta iya nema a bata.

A cewar ta, “Muna son mu tabbatar da cewa akwai wajen da masu shayarwa da ke gasar za su iya kasancewa cikin sirri, kuma su mayar da hankali a kan gasar, to amma ina ga wuraren da ake gasar ta Olympic?

Tuliamuk ta ce wurin gasar tseren Sapporo a 2021 ba a tsara shi yadda mata masu shayarwa da ke gasar za su iya kasancewa da jariransu ba amma bayan da aka samu sauyi saboda zafi, ba ta samu damar sha-yarwa a otal din da jaririyarta da mai kula da ita da kuma mijinta suke ba.

“Na je inda za mu yi tseren inda muke da tanti na tawagar ‘yan wasan Amurka, to amma ba wajen da za ka shayar da jariri ko inda za ka tatsi nono amma da zan so na je bandaki na tatsi nonon, to amma lokaci ya kure sai dai da zai yi kyau a ce akwai wani waje na sirri , to amma ba wanda ya yi tunanin cewa za a samu mata masu shayarwa da ke gasar, ” in ji ta.

 

Bukatar neman canji

Terho ta ce hadin kai da aka samu tsakanin hukumar Olympic ta duniya da takwararta ta gasar Paris, shi ya taimaka wajen tabbatar da wannan sauyi, inda gwarzuwar tseren mita 200 ta gasar Olympic, Allyson Felid ta Amurka, wadda a yanzu ta yi ritaya, take kan gaba wajen tabbatar da wadannan sauye-sauye.

Ita ma tauraruwar kokawar judo Clarisse Agbegnenou, wadda ta ci lambar zinariya biyu ta Olympic, ita ma ta nemi a samar da dama ga mata masu shayarwa, a garinta kasancewar ta shayar da jaririyarta, Athena, ita ma.

Amma ba matan ba ne kadai ke wannan fafutuka ta neman canji, tsohuwar ‘yar tseren Amurka, Alysia Montano na daga cikin masu wannan gwagwarmaya, kasancewar ta taba shiga gasar kasa a 2014 a Sac-ramento, lokacin tana da cikin wata takwas.

Montano ta bayyana irin nasarorin da ta samu tare da tawagar Amurka yayin da take da jaririya, da ku-ma iin matsaloli da kalubalen da ta fuskanta a wannan yanayi kuma sakamakon irin kalubalen da ta fus-kanta da kuma na matan da take goya wa baya a wannan fafutuka, Montano, ta ce sauyin da aka samu a gasar Paris 2024, wani ci gaba ne.

Daya daga cikin manyan kalubalen mata masu shayarwa, da ke son amfani da wurin da aka samar na musamman da za su iya zuwa su kwana da jariransu shi ne yadda za su shawa kan hukumomin kasarsu su samar da kudin tafiyar da wurin.

Terho, ta hukumar shirya wasannin Olympic ta duniya, ta ce hukumar na nazarin yuwuwar samar da hakan a wasannin Olympic nan gaba, amma da farko sai an ga irin yadda tsarin ya kasance a gasar ta Par-is.

To amma ga masu fafutuka irin su Montano, akwai bukatar kara azama kafin gasar Olympic ta gaba ta Los Angeles 2028 domin Montano ta ce, za ta so ta ga an samar da wurare na sirri da suka dace a filayen wasanni, inda mata masu shayarwa za su iya zama cikin tsanaki su tatsi nononsu su ajiye domin amfanin jariransu.

Haka kuma tana son ganin an samar da damar da mata masu shayarwa za su iya kasancewa da masu kula da jariransu tsawon lokacin da suke gasar. Tuliamuk, wadda ba ta samu damar shiga gasar Paris 2024 ba saboda rauni, wadda kuma take fatan zuwa gasa ta gaba ta Birnin Los Angeles, LA 2028, tana fatan ganin ta samu tallafin da take bukata, idan ya kasance ta sake haihuwa a lokacin.

Ta ce kasancewar mace mai shayarwa tare da jaririnta, ba abin da yake sauyawa, hasali ma mace na kasancewa cike da kwarin gwiwa a gasa ta ce sun ga abin da iyaye mata za su iya yi idan aka ba su goyon baya dari bisa dari. Ya kamata su ci gaba da wannan fafutuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GasaJariraiOlympicParisTsari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Sani Ne Ya Sa Wasu Ke Karyata Ikirarin Da Na Yi Na Samun Kyautar Motoci 75 -Mai Dawayya

Next Post

Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

Related

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig
Wasanni

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

11 hours ago
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham
Wasanni

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

15 hours ago
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

17 hours ago
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari
Wasanni

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

1 day ago
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 
Wasanni

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

2 days ago
Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool
Wasanni

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

3 days ago
Next Post
Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

Ko Zuwan Mbappe Zai Dusashe Tauraruwar Bellingham A Real Madrid?

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.