• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita

by Sani Anwar and Sulaiman
10 months ago
in Kiwon Lafiya
0
Amfani Da Kayan Marmarin Da Aka Jima Da Yankawa Na Haifar Da Matsala – Likita
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani kwararren likita a Nijeriya, Dakta Ben Ahunonu; ya gargadi ‘yan Nijeriya kan amfani da kayan marmarin da aka jima da yankawa da ake sayarwa a kan hanya.

 

Likitan ya kara da cewa, wadannan kayan marmari da suka hada da Abarba, Gwanda, Kankana da sauran makamantansu; ana yankawa ana sayarwa a kan titina da sauran hanyoyi, wadanda kuma sanin kowa ne kwari kamar irin su Kuda na bin su; a duk ire-iren wadannan gurare da ake gudanar da wannan sana’a.

  • Baturiya Mafi Tsufa A Duniya Ta Rasu
  • Jawabin Tinubu Kan Kisan Sarkin Gatawa Ya Bar Baya Da Ƙura

“Yanka ire-iren wadannan kayan marmari ana sayarwa, na tattare da matsaloli da dama; musamman ganin cewa ana yanka kayan itatuwan su jima kafin a yi amfani da su, wasu tun safe ake yankawa; haka za su kai har dare, wasu ma su kwana su kara kwana; sannan a haka za a sayarwa da mutane.”

 

Labarai Masu Nasaba

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Saboda haka a cewar tasa, akwai wasu kwayoyin cuta da ke tattare da irin wadannan kayan marmari; sakamakon barin su da ake yi su jima a ajiye bayan an yanka su.

 

“Kudajen da ke bin wadannan kayan marmari, na iya kasancewa ko dauke da wasu kwayoyin cuta; wadanda ka iya haifar da wasu cututtuka kamar; gudawa, ciwon zazzabi (typhoid) da kuma cutar kwalara”, a cewar Daktan.

 

Don haka, sai ya ba da shawarar cewa; cin dukkanin ‘ya’yan itatuwa ko kayan marmari, abu ne da ya kyautu a kula da shi tare da yin nazari sosai; musamman ta fuskar sanya kudi wajen saya da kuma yin la’akari da amfaninsa a jiki.

 

“Saboda galibi bayan an yanka su; iska ta gama ratsa jikinsu, babu wuya suke fara daukar hanyar lalacewa.

 

“Mafi yawan mutane, ba su da ilimin cewa; bawon jikin ‘ya’yan itatuwa su ne ke kare dukkanin abin da ke cikinsu, da zarar an yanka; babu kuma abin da zai kare abin da ke ciki. Shi yasa ake ba da shawarar cewa, ka da a yanka sai an tashi amfani da shi”, in ji shi.

 

Saboda haka, ya sake shawartar mutane da cewa; duk yayin da suka tashi sayen kayan marmari, wajibi ne su duba tare da tabbatar da cewa; bai lalace ba. Dalili kuwa, dukkan kayan marmari masu kyau; wadanda kuma aka yanka nan take, su ne ke da amfani tare da gina jiki.

 

Har ila yau a cewar likitan, kayan itatuwar da aka riga aka yanka; amfaninsu na raguwa idan ba a yi amfani da su nan take ba. Ma’ana, idan aka yanka aka bari suka dauki wani tsawon wani lokaci ba a ci ko an sha ba, amfaninsu na samun koma baya; idan aka kwatanta da wanda aka yanka, aka yi amfani da shi nan take.

 

Haka nan, idan aka ji ya fara canzawa ta fuskar dandano ko warinsa; a nan ya zama wajibi a zubar da shi, ka da a yarda a ci ko a sha.

 

A karshe, ya yi nuni da cewa; idan so samu ne, gwara mutum ya sayi kwallon kayan itatuwar da yake bukata; amma sakamakon matsalar tattalin arziki da ake fuskanta a halin yanzu, mutum zai iya tsayawa ya kula sosai da yanayin wurin da zai sayi wanda aka yanka din tare kuma da duba nagartar wanda zai saya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mashawarcin Shugaban Amurka Kan Harkokin Tsaro Jake Sullivan Zai Ziyarci Kasar Sin 

Next Post

Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Related

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani
Kiwon Lafiya

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

1 week ago
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
Kiwon Lafiya

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

1 week ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

4 weeks ago
Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna
Kiwon Lafiya

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

1 month ago
Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta
Kiwon Lafiya

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

2 months ago
Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam
Kiwon Lafiya

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

2 months ago
Next Post
Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

Gyaran Gashi Ya Yi Kyau Da Laushi

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.