ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Boko Haram Na Ci Gaba Da Tuba A Kasar Nijar

by Sulaiman
1 year ago
Boko Haram

A ci gaba da nasara da ake yi kan mayakan Boko Haram a kasashen Nijeriya, Chadi, Kamaru, da Nijar, an sake samun wasu daga cikin ‘yan bindigar da su ka mika wuya a yankin Diffa na Jamhuriyar Nijar.

 

‘Yan Boko Haram na ci gaba da tuba a Jihar Diffa da ke gabashin Jamhuriyar Nijar da ma sauran wuraren na gabashi, inda a yanzu haka mahukunta ke cigaba da karbar tubabbun mayakan Boko Haram din wadanda suka mika wuya bisa radin kansu, a wani mataki na sake saka su a cikin al’umma amma bayan horas da su ta hanyar sauya musu tunani zuwa mai kyau.

ADVERTISEMENT
  • Babban Kwamandan Boko Haram Da Wasu Mutane 9 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno
  • NIREC Ta Buƙaci Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Rashin Tsaro A Nijeriya

Yanzu an sake samun ‘yan Boko Haram sama da 700 da su ka tuba. Wadannan tubabbun dai a halin yanzu na gudanar mu’amalar zamantakewarsu tsakaninsu da al’umma, inda sannu a hankali su ke sabawa da rayuwar yau da kullum baya ga horas da su din da za a yin a musamman.

 

LABARAI MASU NASABA

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Jihar ta Diffa, wacce ke makotaka da Nijeriya, Chadi, ta yi fama da hare-haren Boko Haram a shekarun da su ka gabata, al’amarin da ya yi sanadin mace- macen mutane da dama ciki har da yara kanana da mata.

 

Wannan ya sa da dama daga cikin ‘yan yankin sun gudu zuwa wasu sassan kasar, baya ga wadanda su ka ketara zuwa wasu kasashe makobta.

 

Idan za a iya tunawa dai, a jihar ta Diffa tun a shekara ta 2015 aka fara rikicin Boko Haram, lokacin da har ta kai ga hukumomin yankin na ta kokarin yin yarjejeniyoyin sulhu da ‘yan Boko Haram. Bayan da aka fara cimma jituwa, sai ‘yan bindigar Boko Haram din suka fara mika wuya a 2016, inda nan take aka shiga tura su a wata cibiyar da ke sake daidaita hankalinsu jihar ta Diffa.

 

A shekara ta 2019 kuwa mahukuntan Jihar Diffa na lokacin suka umurci fara tura tubabbun zuwa ga ‘yan uwansu.

 

Malam Kyari Ari, daya daga cikin tubabbun farko da suka aje makamansu a Jihar Diffa, kuma kawo yanzu suke zaman lafiya da jama’a, ya bayyana cewa an yaudare su ne suka shiga Bako Haram. Ya yi kira ga hukumomi da su taimaka musu da abin yin sana’a don samun abin zaman gari.

Su ma mutanen gari sun bayar da kyakkyawar shaida kan tubabban ‘yan Boko Haram din da cewa suna cikakken zaman lafiya da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna
Manyan Labarai

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Next Post
Haɗarin Kwale-kwale Ya Sake Ajalin Mutane 5 A Jigawa

Haɗarin Kwale-kwale Ya Sake Ajalin Mutane 5 A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.