• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi A Ƙara Ƙulla Danƙon Zumunci A Tsakanin Nijeriya Da Kamfanin BBC

by Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Nemi A Ƙara Ƙulla Danƙon Zumunci A Tsakanin Nijeriya Da Kamfanin BBC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira da a zurfafa alaƙa tsakanin Nijeriya da BBC domin samar da al’umma mai masaniya a kan harkokin yau da kullum.

 

Idris ya bayyana haka ne a wata ziyara da ya kai hedikwatar BBC da ke birnin Landan.

  • An Bude Baje Kolin Manyan Bayanai Na Kasa Da Kasa A Kasar Sin
  • NCC Ta Tsawaita Haɗa Lambar NIN Da Layukan Waya Zuwa Watan Satumba

Ziyarar dai wani ɓangare ne na ƙoƙarin samar da kyakkyawar alaƙa tsakanin Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Nijeriya da kafafen yaɗa labarai daban-daban, na gida da waje.

 

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

A ziyarar,  an yi nasarar ganawa da manyan shugabannin BBC, ciki har da Mataimakin Shugaban Sashen Yaɗa Labarai na BBC kuma Daraktan BBC, Jonathan Munro.

 

Idris ya jaddada muhimmancin kafafen yaɗa labarai wajen tsara fahimtar jama’a da haɓaka ci gaba.

 

Ya ce: “Kafofin watsa labarai suna taka rawa mai muhimmanci wajen tsara labaran da suka dace, da samar da fahimtar juna, da samar da cigaba, don haka ya zama wajibi ga kafafen yaɗa labarai da ke isar da saƙo ga duniya su zurfafa fahimtar yanayin zamantakewa da siyasa da tattalin arziki da al’adun al’ummomin da suke ba da rahoto akai.”

 

Idris ya kuma bayyana muhimmancin rawar da BBC ke takawa wajen bayar da rahotanni kan tafiyar siyasar Nijeriya, yana mai cewa yana da muhimmanci BBC ta daidaita rahotannin da take yi kan Nijeriya ta hanyar mai da hankali kan cigaban da ƙasar ke samu.

 

Ya ƙara da cewa, “Nijeriya tana da ɗimbin matasa masu tasowa da ƙaunar da ba a saba gani ba na cin gajiyar damarmaki ko da kuwa ana fuskantar ƙalubale masu tarin yawa, lamarin da ke buƙatar a ba da muhimmanci ga sakamako mai kyau a Nijeriya.”

 

Ya kuma yi nuni da cewa yaɗa labaran ƙarya babbar matsala ce da ke kawo cikas ga cigaba da kuma lalata amanar da ke tsakanin gwamnati da jama’a.

 

Idris ya yi kira ga BBC da ta yi aiki tare da abokan hulɗar ta na ƙasa da ƙasa don magance waɗannan matsalolin.

 

Ministan ya yaɓa da yadda BBC ke faɗaɗa ayyukan su a Nijeriya ta hanyar samar da ƙarin yarurrukan da suke gabatar da shirye-shirye da su, wato Hausa, Ibo, Yarbanci, da Pijin.

 

Ya ce hakan ya taimaka wajen yaɗa bayanai da yawa tare da samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin APCKafafen Yada LabaraiMinistan Yaɗa Labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tawagar Jami’an Jihar Guangxi Ta Sin Ta Ziyarci Kasar Niger

Next Post

‘Yansanda Sun Yi Allah-Wadai Da Kisan Gillar Da Sojoji Suka Yi Wa DPO Wasagu A Kebbi

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

2 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

4 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

5 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

9 hours ago
Next Post
Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda

‘Yansanda Sun Yi Allah-Wadai Da Kisan Gillar Da Sojoji Suka Yi Wa DPO Wasagu A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.