• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafin Lantarki Ga Asibitoci Da Manyan Makarantu Ka Iya Lakume Naira Biliyan 188

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Tallafin Lantarki Ga Asibitoci Da Manyan Makarantu Ka Iya Lakume Naira Biliyan 188
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ka iya kashe a kalla naira biliyan 188.25 a kowace shekara wajen biyan tallafin kudi na wutar lantarki ga asibitocin gwamnati sama da 75 da manyan makarantu su 300 a sassan kasar nan.

Wannan na zuwa ne biyo bayan amincewa da gwamnatin tarayya ta yi da sassaucin kaso 50 cikin 100 na kudin lantarki ga asibitocin gwamnati da kuma manyan makarantu a fadin Nijeriya.

  • Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Zuwa Jana’izar Mahaifiyar Yar’Adua
  • Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

A watan Afrilu ne hukumar kula da wutar lantarki ta sanar da karin kudin wutar lantarki ga masu amfani da rukunin A na karin kudi da aka samu da kaso 300.

Tun da farko dai, ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya yi alkawarin cewa gwamnatin tarayya za ta tallafa wa asibitoci da manyan makarantun da suke mallakinta wajen rage musu kudin wutar lantarki da suke biya.

Ya ce, gwamnati tana sane da irin kudin da asibitoci da manyan makarantu ke kashe wajen biyan kudin wuta, wanda hakan ya zama musu babban kalubale.

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Karamin ministan lafiya, Dakta Tunji Alausa, ya sanar a ranar Alhamis cewa gwamnatin tarayya ta amince da biyan tallafin lantarki na kaso 50 ga asibitocin gwamnati.

A cewar Alausa, wannan an yi ne domin rage wa asibitocin kashe maguden kudade wajen biyan kudin wuta wanda hakan ke shafar majinyata da ya sanya ake cazansu kudi da yawa.

Binciken da majiyarmu ta gudanar, ya nuna cewa gwamnatin tarayya za ta iya kashe naira miliyan 50 ga kowace asibiti daga cikin sama da 75, inda ya kai kimanin biliyan 3.75 a kowace wata, wato biliyan 45 a shekara guda.

Shugaban kwalejin fasaha ta Yaba da ke Legas, Dakta Ibraheem Abdul, ya yaba wa gwamnatin tarayya bisa wannan, yana mai cewa tabbas hakan zai taimaka wajen kyautata koyarwa da kuma rage wa makarantu tsula kudi ga dalibai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsibitiBola Ahmed TinubuNepaPower
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Kaddamar Da Sassakar Tunawa Da Gasar Olympics Ta Paris 

Next Post

Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

2 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

3 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar É—orewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar É—orewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

8 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

10 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

10 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

13 hours ago
Next Post
Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

Ta Yaya Sin Da Afirka Za Su Ci Moriyar Juna Ta Fuskokin Tattalin Arziki D Kasuwanci?

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

August 1, 2025
Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

Sin Ta Samarwa Sassan Kasa Da Kasa Damar Shigowa Ba Tare Da Bukatar Biza Ba

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.