ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

by Abubakar Abba
2 years ago
Filato

A kokarinta na samar da mafita, ga ‘yan gudun hijira, gwamnatin tarayya ta kaddamar da aikinta na tallafa wa aikin aikin noma da ake kira ‘REHAEP’ ga ‘yan gudun hijirar da ke zaune a Jihar Filato, a sansaninsu na yankin Kpwasho a Karamar Hukumar Bassa ta jihar.

Har ila hau, aikin hadaka ne tsakanin hukumar kula da bakin haure da ‘yan gudun hijira ta kasa da kasa (NCFRMI) da kuma ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci.

  • Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu
  • Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba

Kwamishinan hukumar, Tijjani Ahmed ya bayyana cewa; an ware gona mai fadin kadada 150, domin gudanar da wannan aiki, inda ya kara da cewa, ‘yan gudun hijira 300 za a tallafawa da kayan aiki da kuma tallafin kudi.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, Ahmed ya kara da cewa; su ma masana’antu masu zaman kansu, za su taimaka wajen tabbatar da ganin an yi girbin amfanin gonan da ‘yan gudun hijirar suka noma, wanda hakan zai taimaka wajen kara samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

Ya ci gaba da cewa, an wanzar da wannan aiki na gwaji a Jihohin Nasarawa da Borno, wanda kuma aka shirya fadada shi zuwa sauran jihohin kasar nan, har zuwa shekara biyar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

A cewar Ahmed, za a shuka Irin noma kamar na Shinkafa, Masara, Dawa, Alkama da sauransu a cikin wadannan kadada 150.

Sanna kuma ya ce, ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, za ta samar da kayan aiki, domin noma hekta 150, inda kuma hukumar NCFRMI za ta samar da tallafin kudade ga ‘yan gudun hijirar.

Ahmed, wanda Darakata ne a hukumar; Fatima Mamman Daura ita ce ta wakilce shi tare da bayyana cewa, hukumar ta kuma yi hadaka da rundunar  tsaron farin kaya ta NSCDC da ke bai wa manoma kariya,

Shi kuwa gwamnan jihar, Caleb Muftwang a nasa jawabinn ya ce, ya kamata manoma a jihar su rika yin noma mai yawa, inda ya kara da cewa; gwamnatinsa za ta tallafa wa wadannan ‘yan gudun hijira.

Muftwang, wanda shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa na jihar ‘PLASSIMA’, Mista Sunday Audu ya wakilta a wajen taron ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa za ta tabbatar da an mayar da ‘yan gudun hijirar ga matsugunansu tare da magance kalubalen karatun ilimin boko na ‘ya’yansu.

A cewar tasa, a yanzu haka akawai hadakar da ake ci gaba da yi da jami’an tsaro da rundunar tsaron farin kaya ta NSCDC, domin karfafa tsaro a gonakan manoman ta yadda za su yi nomansu ba tare da jin wani tsoron harin ‘yan bindiga ba.

Filato
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.