ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Ƙaddamar Da Aikin Noma Ga ‘Yan Gudun Hijira A Filato

by Abubakar Abba
2 years ago
Filato

A kokarinta na samar da mafita, ga ‘yan gudun hijira, gwamnatin tarayya ta kaddamar da aikinta na tallafa wa aikin aikin noma da ake kira ‘REHAEP’ ga ‘yan gudun hijirar da ke zaune a Jihar Filato, a sansaninsu na yankin Kpwasho a Karamar Hukumar Bassa ta jihar.

Har ila hau, aikin hadaka ne tsakanin hukumar kula da bakin haure da ‘yan gudun hijira ta kasa da kasa (NCFRMI) da kuma ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci.

  • Sabon Matakin FOCAC Na Jagorantar Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Wajen Zamanintar Da Al’umomminsu
  • Dalilin Da Ya Sa Makiyaya Suka Tafka Asarar Shanu Sama Da 1,000 A Taraba

Kwamishinan hukumar, Tijjani Ahmed ya bayyana cewa; an ware gona mai fadin kadada 150, domin gudanar da wannan aiki, inda ya kara da cewa, ‘yan gudun hijira 300 za a tallafawa da kayan aiki da kuma tallafin kudi.

ADVERTISEMENT

Haka zalika, Ahmed ya kara da cewa; su ma masana’antu masu zaman kansu, za su taimaka wajen tabbatar da ganin an yi girbin amfanin gonan da ‘yan gudun hijirar suka noma, wanda hakan zai taimaka wajen kara samar da wadataccen abinci a fadin kasar nan baki-daya.

Ya ci gaba da cewa, an wanzar da wannan aiki na gwaji a Jihohin Nasarawa da Borno, wanda kuma aka shirya fadada shi zuwa sauran jihohin kasar nan, har zuwa shekara biyar.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

A cewar Ahmed, za a shuka Irin noma kamar na Shinkafa, Masara, Dawa, Alkama da sauransu a cikin wadannan kadada 150.

Sanna kuma ya ce, ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, za ta samar da kayan aiki, domin noma hekta 150, inda kuma hukumar NCFRMI za ta samar da tallafin kudade ga ‘yan gudun hijirar.

Ahmed, wanda Darakata ne a hukumar; Fatima Mamman Daura ita ce ta wakilce shi tare da bayyana cewa, hukumar ta kuma yi hadaka da rundunar  tsaron farin kaya ta NSCDC da ke bai wa manoma kariya,

Shi kuwa gwamnan jihar, Caleb Muftwang a nasa jawabinn ya ce, ya kamata manoma a jihar su rika yin noma mai yawa, inda ya kara da cewa; gwamnatinsa za ta tallafa wa wadannan ‘yan gudun hijira.

Muftwang, wanda shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa na jihar ‘PLASSIMA’, Mista Sunday Audu ya wakilta a wajen taron ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa za ta tabbatar da an mayar da ‘yan gudun hijirar ga matsugunansu tare da magance kalubalen karatun ilimin boko na ‘ya’yansu.

A cewar tasa, a yanzu haka akawai hadakar da ake ci gaba da yi da jami’an tsaro da rundunar tsaron farin kaya ta NSCDC, domin karfafa tsaro a gonakan manoman ta yadda za su yi nomansu ba tare da jin wani tsoron harin ‘yan bindiga ba.

Filato
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

NNPC Ya Karyata Batun Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Binsa Bashin Dala Biliyan 6

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.