ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afrika Ta Kudu Na Neman Hadin Gwiwa Da Sin Wajen Zamanantar Da Kanta

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afrika

Babbar jami’ar jam’iyyar ANC mai mulkin Afrika ta kudu, ta ce kasar Sin ta samu gagarumar nasara a kan tafarkinta na zamanantar da kanta, kuma Afrika ta Kudu na ganin akwai dimbin damarmakin hadin gwiwa da Sin wajen inganta zamanantar da kanta. 

 

Gwen Ramokgopa, wadda ita ce babbar ma’ajiya ta jam’iyyar ANC, ta ce dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika (FOCAC), ya cimma kyakkyawan sakamako ta hanyar shirye-shiryen hadin gwiwar moriyar juna.

ADVERTISEMENT
  • ’Yan Kasuwa Daga Kasashe Da Yankuna 119 Sun Halarci CIFIT Karo Na 24 
  • Dubban Jama’a A Isra’ila Sun Yi Zanga-Zangar Neman Amincewa Da Yarjejeniyar Hamas

Ta ce taron FOCAC, ya kasance wata muhimmiyar dama ta karfafa hadin gwiwar Sin da Afrika a bangarori da dama, musammam a bangaren bunkasa dangantakar tattalin arziki da cinikayya .

 

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Taken taron wanda ya gudana daga ranar Laraba zuwa Jumma’a, shi ne “hada hannu domin inganta zamanantarwa da gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya bisa babban mataki.”

 

Ta ce idan ana son inganta zamanantar da nahiyar Afrika, akwai bukatar la’akari da albarkar tattalin arzikin nahiyar da yadda za a lalubo damarmakin ci gaba da nahiyar ke da shi, wanda ke nufin kirkiro kyakkyawan muhallin kasuwanci da inganta hidimtawa al’ummar nahiyar da amfana da sabbin fasahohi, ciki har da fasahohi masu tsafta da suka shafi makamashi da motoci masu amfani da lantarki, tana mai cewa, Sin ta kasance jagora a wadannan bangarori, don haka, akwai damarmakin da za a iya karfafa hadin gwiwa da ita don daukaka zamanantar da kasar ta Afrika ta Kudu.

 

Ta kuma yaba sosai da shawarwarin taimakawa nahiyar Afrika bunkasa ayyukan masana’antu da shirin Sin na zamanantar da aikin gona a Afrika da shirin hadin gwiwar Sin da Afrika kan horar da masu basira, wadanda kasar Sin ta gabatar.

 

A cewarta, Sin da Afrika ta Kudu mambobi ne na kungiyar BRICS, kuma wakilan kungiyar kasashe masu tasowa, don haka, hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu a mabambantan dandamali, ya taimaka wajen kara sautin muryar kasashe masu tasowa. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Xi Ya Rattaba Hannu Kan Umarnin Amfani Da Ka’idojin Kare Muhalli A Aikin Soja

Xi Ya Rattaba Hannu Kan Umarnin Amfani Da Ka’idojin Kare Muhalli A Aikin Soja

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.