• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaƙi Da ‘Yan Bindiga: Yadda Gwamna Dauda Ya Karɓi Baƙuncin Babban Hafsan Tsaro

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Bindiga

Gwamna Dauda Lawal ya tabbatar wa rundunar sojojin ƙasar nan jajircewar gwamnatinsa wajen bai wa jami’an soji cikakken goyon bayan gwamnatin sa a jihar Zamfara. 

 

Ranar Juma’ar da ta gabata, Gwamna Lawal ya karɓi baƙuncin Babban Hafsan tsaron ƙasa (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa a tsohon ɗakin taron fadar gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 40 A Hatsarin Kwale-kwale
  • Bukukuwan Mauludi: Wani Mummunan Hatsari Ya Ci Rayukan Mutane 40 A Saminaka

Sanarwa daga mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ta bayyana cewa Babban Hafsan tsaron ya sanar da wani laƙabi da za a rinƙa kiran rundunar haɗin gwiwa ta yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Yamma, inda ya ce za a rinƙa kiranta da ‘rundunar samamen Fansan Yamma, wanda kuma yanzu ita ce rundunar da aka sani a yankin Arewa maso Yamma.

 

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sanarwar ta ci gaba da cewa, wannan runduna ta ‘Operation Fansan Yamma,’ wani laƙabi ne da ke nuni da cewa jami’an tsaron a shirye su ke don ganin sun murƙushe harkar ‘yan bindiga a yankin na Arewa maso Yamma.

 

Cikin jawabin sa, Gwamna Dauda ya yaba wa Babban Hafsan bisa irin namijin ƙoƙarin da ya ke yi wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan.

Bindiga

“Janar, kasancewarka a Zamfara a wannan lokaci, ya ƙara ƙara wa jami’an soji ƙwarin gwiwa. Ka ƙara tabbatar da fatan mu, al’umma na cike da fata.

 

“Ba za mu taɓa yin wasa da wannan ziyara ba. Gwamnatina ta jajirce wajen haɗa kai da Hukumomin tsaro don tabbatar da tsaro a jihar Zamfara.

 

“Bisa la’akari da jawabinka, ina da tabbacin cewa zaman lafiya zai dawo a Zamfara. Ka yi makaranta a nan, ka san irin yanayin zaman lafiyar da ake da shi a da. Gusau ta kasance birni na biyu a harkar Kasuwanci a Arewa bayan jihar Kano.

 

“Na ji daɗin kasacewa kana aiki tare da rundunar Askarawan Zamfara ta CPG. Ina so ka sani, kafin a zaɓi Askarawan Zamfara sai da Hukumar tsaro ta DSS da sauran hukumomin tsaro suka tantance su.

 

“Muna bayar da cikakken goyon bayan mu ga sojoji a ƙoƙarin su na yaƙi da ‘yan bindiga. An tura waɗannan jami’ai zuwa yankunan su. Muna da yaƙinin cewa sojoji a jajirce suke wajen magance matsalar tsaro.

 

“Zan yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta’aziyyata bisa jajirtattun jami’an da suka rasu a hanyar Gusau zuwa Funtuwa. Allah gafarta masu. Ina tabbatar maka da cewa gwamnatina na tare da kai, kuma za mu ci gaba da aiki tare da jami’an soji da sauran hukumomin tsaro don kawo ƙarshen ‘yan bindiga.”

Bindiga

Tun farko a jawabinsa, Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, ya nuna matuƙar godiyar sa ga Gwamna Dauda Lawal bisa goyon bayan da ya ke bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro a jihar. “Mun zo nan ne don muna godiyar mu bisa irin goyon bayan da ka ke bai wa sojoji da sauran jami’an tsaro, tare da irin gagarumar ci gaban da kake samarwa a jihar Zamfara.

 

“Na kasance ina alfahari da Gusau da na sani, amma gaskiya, yanzu abin da na gani, sai na rasa me zan ce. Yabon gwani ya zama dole bisa irin ci gaban da ka samar wa Zamfara a shekara ɗaya kacal, a ƙarƙashin jagorancinka. Ina gode maka bisa inganta rayuwar al’umma. Wannan romon Dimokraɗiyya ne. Muna ganin ci gaba da dama, tare da wasu ayyukan da ake gudanarwa a jihar, tun bayan hawan ka mulki.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

WIPO Ta Yabawa Gudunmuwar Kasar Sin Wajen Tabbatar Da Hakkin Mallakar Fasaha  

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.