• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Yi Wa Almajiri Fyade: Masu Kare Hakkin Dan’adam Sun Sake Shigar Da Kara

by Abubakar Abba
12 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Kotu Ta Hana Miji Magana Da Matarsa Tsawon Mako Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu masu kare hakkin ‘yan Adam a Jihar Kaduna sun shigar da kara a gaban kotun Majistari da ke da zama a titin Daura Road, mai lamba 37.

Sun shigar da karar ce, don kotun ta sake bude shari’ar yaron nan Almajiri dan shekara 13 da wani mai suna Isah Abdullah daya daga cikin hadimin ‘yar majalsair dokin jihar Kaduna Munirat Suleiman mai wakilitar mazabar Saminaka ya yi wa fyade.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i
  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC

A cewasu, ba su amince da wancan hukukuncin da alkalin kotun Majistari mai lamba 2 Mai Shari’a Aliyu Dogara ya yanke na wanke Isah Abdullah da kuma sakinsa ba.

Idan za a iya tunawa, binciken da sashin manyan laifuka na rundunar ‘yansandan a Jihar Kaduna ya yi, a kan zargin ya gabatar da Isa gaban kotun mai lamba 2, wanda kotun ta bayar da umarni a ajiye Isah a gidan gyaran hali na jihar, kafin ma’aikatar Shari’ar jihar ta bayar da shawara a kan zargin.

Amma bayan jiran shawara daga ma’aikatar Shara’a ta jihar, ta wanke Isa a sakamakon rahoton gwaji da aka samu daga Asibiti a Saminaka da kuma Asibitin koyarwa na Barau Dikko.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Sai dai, masu kare rajin hakkin ‘yan’adam a jihar, sun bayyana cewa, ba su amince da wancan hukuncin kotun da kuma takardun gwajin lafiyar yaron da Asibitin Barau Dikko da Garin Saminaka suka yi a kan Almajirin ba, inda suka sake garzayawa kotun ta Majistari da ke mai lamba 37, don ta bude Shari’ar.

A hirarsa da ‘yan jarida a Kaduna daya daga cikin masu kare rajin Marwan Yabo ya ce, wancan hukuncin da kotun Daura Road mai lamba 2 ta yanke bamu yarda da shi ba.

A cewarsa, masu kare wanda ake zargin a gaban kotun, sun yi amfani da wasu takardun da aka yiwa yaron gwaji ne, a wani Asibiti da ke a Saminaka da kuma gwajin da aka yi, a Asibitin Barau Dikko, kuma takardun gwajin da aka yi, a wadannan Asibitocin biyu, na hannun mu.

Ya ci gaba da cewa, akwai kuma wasu takardu biyu wadanda suke nuna cewa, wai daga Asibitin Saminaka da kuma na Barau Dikko ne, aka bayar.

Ya kara da cewa, “To amma bamu san yadda aka yi suka samo wadannan takardun biyu ba, domin Asibitin Barau Dikko, a baya da kansu ne suka yi wa yaron gwaji suka kuma tura shi zuwa Asibitin kashi na Dala, da ke a Kano don a yi wa yaron aiki”.

Ya ce, bayan kotun mai lamba 2 ta bayar da umarnin cewa, a ajiye Isah a gidan gyran hali na jihar har sai yaron ya samu lafiya kafin a fara shari’ar, sai kawai muka ji cewa, wai kotun mai lamba 2 ta wanke Isah daga zargin, alhali ba a ma fara shariar gadan-gadan ba, kuma ba ji ta bakin yaron a kan me ya faru ba.

Shi ma daya mai kare hakiin ‘yan’adam kuma lauyan yaron Barista Sani Shehu a zantawarsa da ‘yanjarida ya ce, za su tabbatar an binciki wancan hukuncin da kotun mai lamba 2 ta yanke, inda ya kara da cewa,”Muna zargin akwai shubuha a cikin hukuncin da kotun mai lamba 2 ta yanke”.

Ya ce, idan har ita ma’aikatar shari’a ta kamar yadda takardun suka nuna cewa, ta dogara ne da wasu takardu na likita wadanda mai yiwuwa, wadancan takardun na likitan an kawo su ne ta bayan fage, ma’aikatar kuma ta yi abin da ta yi, doka ta bamu damar muma mu sake bude wata sabuwar shari’a.

Ya ce, ita kuma kotun da ta wanke wanda ake zargin, “Muna da ikon mu nemi kotu ta sama, ta warware wancan hukuncin na kotun ta 2, don a sake wani bincike don mu gabatar da dalilanmu”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FyadeKadunaKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Tsohon Alkali A Kotu Kan Zargin Lakada Wa Matar Aure Duka

Next Post

Matafiyi Obobo Ya Rasu

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
Next Post
Matafiyi Obobo Ya Rasu

Matafiyi Obobo Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

September 14, 2025
Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.