• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa ‘Yan Wasa Suka Fara Korafi A Kan Yawan Wasannin Da Suke Bugawa?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Me Ya Sa ‘Yan Wasa Suka Fara Korafi A Kan Yawan Wasannin Da Suke Bugawa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ba wannan lokacin bane ‘yan wasan kwallon kafa a duniya suka fara korafi a kan yawan wasannin da suke bugawa wanda hukumomin kwallon kafa na FIFA da EUFA suke kara musu a kan wadanda suke bugawa a baya.

Tun a shekarun baya tsohon kociyan Real Madrid da Manchester United, Jose Mourinho, ya yi korafi a kan yawan wasannin da ake sake karawa ‘yan wasa wanda hakan a cewarsa yana kawo gajiya ga ‘yan wasan kuma baya taimaka musu.

  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC
  • Sarakuna 2 A Kano: Ina Aka Kwana?

Tsohon kociyan Liberpool, Jugen Klopp, da na Manchester City, Pep Guardiola, sun yi korafi a kan yawan wasannin da hukumomi suke karawa wanda hakan yana kawo yawan jin ciwo da rashin kuzari ga ‘yan wasa.

A farkon wannan watan ne shima dan wasan Manchester City da kasar Belgium, Kebin de Bruyne, ya yi korafi a kan cewa suma mutane ne kamar kowa saboda haka wasannin da ake sake karawa sun yi yawa soasai.

Shima dan wasan Manchester City, Rodri ya ce ‘‘yan wasan na dab da yin yajin aiki, sakamakon da aka kara yawan wasannin da za suke bugawa wanda a cewarsa ya kamata a dinga tuntubarsu idan za a kara yawan wasanni saboda su ne suke bugawa.

Labarai Masu Nasaba

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Manchester City ta kara da Inter Milan ranar Laraba a Champions League, wanda aka kara wasa biyu kafin karawar zagaye na biyu a sabon fasalin babbar gasar Zakarun Turai ta bana wanda aka fara a ranar 17 ga wannan watan.

A gasar Club World Cup kuwa, inda Manchester City za ta fafata daga badi, an kara kungiyoyi sun kai 32, an samu karin wasanni da yawa kenan wanda hakan ne ya sa dan wasa Rodri ya ce yana jin suna dab da yin yajin aiki.

Ya ci gaba da cewa idan har an ci gaba da haka, za a kai lokacin da ba su da wani zabi sai dai kawai su tsunduma yajin aiki saboda suma mutane ne kamar kowa kuma suna da iyali kamar kowa amma za su dan kara jira su gani.

A sabon fasalin Champions League da Club World Cup na nufin Manchester City za ta buga karin wasanni hudu a kakar daga bana, fiye da yawan da ta fafata a bara wanda hakan zai kasance ‘yan wasa za su gaji sosai. Wasanni biyu kacal Manchester City ta yi ta kuma lashe Club World Cup a Disamba, amma a kakar badi za ta yi karawa uku a cikin rukuni da hudu a zagayen gaba har kai wa karawar karshe kuma a kakar wasa biyu baya,

Manchester City ta buga wasanni 120 a dukkan fafatawa, yayin da Rodri ya buga wasanni 63 a kwanaki 343 a kakar wasa ta 2023 zuwa 2024.

Rodri, wanda ya buga wa tawagar Sifaniya da Manchester City wasa 63 a bara, ya lashe Premier League da kofin Nahiyar Turai da ya buga cikin wata biyu kuma bayan tashi daga Champions League karawar dab da karshe a gidan Real Madrid, Rodri ya sanar a cikin watan Afirilu cewar yana bukatar hutu.

Hakan ne ma ya sa bai buga wa Manchester City wasanni uku da fara kakar bana ba, ya fara daga 2-1 inda ta doke Brentford a Premier League ranar Asabar, kwana shida tsakani da ya yi wa Sifaniya Nations League.

Bayan kammala kakar wasa ta 2023 zuwa 2024 wadda aka fara daga 6 ga watan Agustan shekarar 2023 da aka kammala a kwana 343, ranar 14 ga watan Yuli, Rodri ya sanar cewar yana bukatar dogon hutu fiye da wanda ake bashi.

Masana suna ganin yawan ciwon da wasu ‘yan wasan suke samu yana da alaka da yawan wasannin da suke bugawa domin ban da wasannin kungiyoyinsu, ‘yan wasan suna wakiltar kasashensu a wasannin gasa daban-daban ko kuma wasannin sada zumunta ko kuma na neman cancantar shiga gasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaKorafiWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Su Waye ‘Yan Afirka Da Suka Canja Kungiya A Turai?

Next Post

Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

Related

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or
Wasanni

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

1 day ago
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya
Wasanni

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

1 day ago
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya
Wasanni

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

1 day ago
Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya
Wasanni

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

2 days ago
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

4 days ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

5 days ago
Next Post
Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.