ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa ‘Yan Wasa Suka Fara Korafi A Kan Yawan Wasannin Da Suke Bugawa?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Wasa

Ba wannan lokacin bane ‘yan wasan kwallon kafa a duniya suka fara korafi a kan yawan wasannin da suke bugawa wanda hukumomin kwallon kafa na FIFA da EUFA suke kara musu a kan wadanda suke bugawa a baya.

Tun a shekarun baya tsohon kociyan Real Madrid da Manchester United, Jose Mourinho, ya yi korafi a kan yawan wasannin da ake sake karawa ‘yan wasa wanda hakan a cewarsa yana kawo gajiya ga ‘yan wasan kuma baya taimaka musu.

  • Xi Ya Jaddada Ba Da Cikakkiyar Dama Ga Fa’idar Siyasa Ta CPPCC
  • Sarakuna 2 A Kano: Ina Aka Kwana?

Tsohon kociyan Liberpool, Jugen Klopp, da na Manchester City, Pep Guardiola, sun yi korafi a kan yawan wasannin da hukumomi suke karawa wanda hakan yana kawo yawan jin ciwo da rashin kuzari ga ‘yan wasa.

ADVERTISEMENT

A farkon wannan watan ne shima dan wasan Manchester City da kasar Belgium, Kebin de Bruyne, ya yi korafi a kan cewa suma mutane ne kamar kowa saboda haka wasannin da ake sake karawa sun yi yawa soasai.

Shima dan wasan Manchester City, Rodri ya ce ‘‘yan wasan na dab da yin yajin aiki, sakamakon da aka kara yawan wasannin da za suke bugawa wanda a cewarsa ya kamata a dinga tuntubarsu idan za a kara yawan wasanni saboda su ne suke bugawa.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Manchester City ta kara da Inter Milan ranar Laraba a Champions League, wanda aka kara wasa biyu kafin karawar zagaye na biyu a sabon fasalin babbar gasar Zakarun Turai ta bana wanda aka fara a ranar 17 ga wannan watan.

A gasar Club World Cup kuwa, inda Manchester City za ta fafata daga badi, an kara kungiyoyi sun kai 32, an samu karin wasanni da yawa kenan wanda hakan ne ya sa dan wasa Rodri ya ce yana jin suna dab da yin yajin aiki.

Ya ci gaba da cewa idan har an ci gaba da haka, za a kai lokacin da ba su da wani zabi sai dai kawai su tsunduma yajin aiki saboda suma mutane ne kamar kowa kuma suna da iyali kamar kowa amma za su dan kara jira su gani.

A sabon fasalin Champions League da Club World Cup na nufin Manchester City za ta buga karin wasanni hudu a kakar daga bana, fiye da yawan da ta fafata a bara wanda hakan zai kasance ‘yan wasa za su gaji sosai. Wasanni biyu kacal Manchester City ta yi ta kuma lashe Club World Cup a Disamba, amma a kakar badi za ta yi karawa uku a cikin rukuni da hudu a zagayen gaba har kai wa karawar karshe kuma a kakar wasa biyu baya,

Manchester City ta buga wasanni 120 a dukkan fafatawa, yayin da Rodri ya buga wasanni 63 a kwanaki 343 a kakar wasa ta 2023 zuwa 2024.

Rodri, wanda ya buga wa tawagar Sifaniya da Manchester City wasa 63 a bara, ya lashe Premier League da kofin Nahiyar Turai da ya buga cikin wata biyu kuma bayan tashi daga Champions League karawar dab da karshe a gidan Real Madrid, Rodri ya sanar a cikin watan Afirilu cewar yana bukatar hutu.

Hakan ne ma ya sa bai buga wa Manchester City wasanni uku da fara kakar bana ba, ya fara daga 2-1 inda ta doke Brentford a Premier League ranar Asabar, kwana shida tsakani da ya yi wa Sifaniya Nations League.

Bayan kammala kakar wasa ta 2023 zuwa 2024 wadda aka fara daga 6 ga watan Agustan shekarar 2023 da aka kammala a kwana 343, ranar 14 ga watan Yuli, Rodri ya sanar cewar yana bukatar dogon hutu fiye da wanda ake bashi.

Masana suna ganin yawan ciwon da wasu ‘yan wasan suke samu yana da alaka da yawan wasannin da suke bugawa domin ban da wasannin kungiyoyinsu, ‘yan wasan suna wakiltar kasashensu a wasannin gasa daban-daban ko kuma wasannin sada zumunta ko kuma na neman cancantar shiga gasa.

Wasa
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

Fashewar Bam Ta Kashe Da Raunata Daruruwan Mutane A Lebanon

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.