ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarakuna 2 A Kano: Ina Aka Kwana?

by Abdullahi Muh'd Sheka
2 years ago
Kano

Kusan shekara guda kenan ake ta yamutsa gashin baki tsakanin wasu jiga-jigai biyu da ake ganin suna ta nunawa juna yatsu kan batun masarautar Kano, wanda a yanzu sarakuna biyu kowane ke kallon kawunansu a matsayin latattun sarakai, tsakanin sarkin na 15 da kuma 16 wanda guda ke cikin gidan Dabo, yayinda dayan kuma ke karamin gidan sarki na Nasarawa.

Idan dai za a iya tuna, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ne ya kafa wani kwamitin da ya binciki zargin da suka yi wa Sarki Muhammadu Sanusi II, wanda suka zarga da yi wa Gwamnatin Ganduje makarkashiya.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Bana Cikin Wani Shiri Na Tsige Sanusi II A Matsayin Sarkin Kano – Ganduje

Bayan faduwar gwamnatin da ake ganin ita ce ta yi sanadiyyar tsige Sarki Muhammadu Sanusi, sai gwamnatin NNPP wadda ke adawa da matakan da aka dauka kan sarki Sanusi ta samu nasarar daman daukar matakin mayar da shi, wanda daman hakan na cikin alkawarin da Kwankwasiyya ta yi, saboda haka ba a dauki lokaci ba sai aka gabatar da bukatar sake duba dokar da majalisar dokokin lokacin Ganduje ta zartar wadda aka yi amfani da ita wajen cire Sanusi II.

ADVERTISEMENT

Bayan shigar da Muhammadu Sanusi II gidan Dabo cikin dare, sai Sarki Aminu ya dawo daga tafiyarsa washegari inda ya wuce karamar fadar da ke gidan Sarki na Nasarawa, wanda tun daga wancan lokacin a karon farko sarakuna biyu ke gabatar da mulkin masarautar ta Kano daga wurare daban-daban.

Babban kalubalen da Sarkin Sanusi ke fuskanta shi ne, rashin samun goyon bayan gwamnatin tarayya, musamman ganin jam’iyyar APC ke mulki, wanda shi kuma Sarki Sanusi jama’a sun gamsu da yadda ya taimaka wajen kayar da jam’iyyar a Kano, saboda alkawarin da Kwankwasawa suka yi masa na dawo da shi kan kargar sarautar Kano.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Sarki Aminu wanda ke samun goyon bayan gwamnatin tarayya da kuma umarnin wasu kotuna guda biyu da hukuncinsu ya tabbatar da shi a matsayin halastaccen sarki, ya kasance yana ci gaba da aiwatar da harkokin mulki daga waccan karamar fadar, tare da fuskantar kalubale daga bangaren Gwamnatin Jihar Kano, wadda har majalisa aka kai bukatar rushe katangar gidan sarkin na Nasarawa da sunan za a gyara gidan.

Sakamakon wannan ne ya sa tsohon gwamnan Kano kuma shugaban jam’iyyar APC na kasa ake ganin yana cikin wadanda suka hana Sarki Sanusi II rawar gaban hantsi, sannan kuma ya toshe duk wata kofa da gwamnatin Kano ka iya samu wajen karfafa mulkin Sarkin Sanusi, sannan akwai kotuna guda biyu duk na gwamnatin tarayya ne wadada hukuncinsu ya bai wa Sarki Aminu gaskiya a shari’un da ke gabansu, saboda haka hukuncin da ake sauraro yanzu shi ne ka iya nuna makomar Sarki Sanusi II da kuma shi kansa Sarki Aminu.

Sai dai kuma daga irin abubuwan da ake gani a duk lokacin da wani daga cikin sarakunan biyu ya fito cikin al’umma, ana iya fahimtar wanda talakawa suka fi sha’awa, musamman duba da dawowar Sarki Sanusi daga kasar Ingila, lokacin ya je kare digirin-digirgir dinsa, yayin da shi kuma sarki Aminu ya halarci taro da aka saba gudanarwa duk shekara a masallachi Marigayi Khalifa Isyaka Rabi’u.

Saboda haka batun da ake na cewa Dakta Ganduje na shirya wata kulalliya domin tabbatar da sallamar Sarki Sanusi II ba wani sabon abu ba ne, domin yana daga cikin alkawuran da gwamnatin Kano ta yanzu ke kansu na yin duk mai yiwuwa wajen rushe duk wani tsari na Ganduje, sannan kuma kusancinsa da shugaban kasa, musamman kasancewarsa shugaban jam’iyyar da Bola Tinubu ya ci zabe karkashin tutarta.

Muhimmancin Jihar Kano a wurin gwamnatin tarayya ya sa wasu ke ganin su Ganduje za su ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen ganin sun hana Sarki Sanusi zama a karaga.

Yanzu haka akwai kishin-kishin cewa, Ganduje ya tattaro mukarabbansa ciki har da ‘yan kasuwa da manyan dattawan jihar domin neman Shugaba Bola Tinubu ya sa baki Sarki Sanusi da Sarki Aminu kowa ya hakura domin samun maslaha.

Sai dai har yanzu abin na nan lullube a cikin duhu wanda lokaci ne kadai iya tabbatarwa.

Kano
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.