• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarakuna 2 A Kano: Ina Aka Kwana?

by Abdullahi Muh'd Sheka
10 months ago
in Labarai
0
Sarakuna 2 A Kano: Ina Aka Kwana?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kusan shekara guda kenan ake ta yamutsa gashin baki tsakanin wasu jiga-jigai biyu da ake ganin suna ta nunawa juna yatsu kan batun masarautar Kano, wanda a yanzu sarakuna biyu kowane ke kallon kawunansu a matsayin latattun sarakai, tsakanin sarkin na 15 da kuma 16 wanda guda ke cikin gidan Dabo, yayinda dayan kuma ke karamin gidan sarki na Nasarawa.

Idan dai za a iya tuna, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ne ya kafa wani kwamitin da ya binciki zargin da suka yi wa Sarki Muhammadu Sanusi II, wanda suka zarga da yi wa Gwamnatin Ganduje makarkashiya.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Bana Cikin Wani Shiri Na Tsige Sanusi II A Matsayin Sarkin Kano – Ganduje

Bayan faduwar gwamnatin da ake ganin ita ce ta yi sanadiyyar tsige Sarki Muhammadu Sanusi, sai gwamnatin NNPP wadda ke adawa da matakan da aka dauka kan sarki Sanusi ta samu nasarar daman daukar matakin mayar da shi, wanda daman hakan na cikin alkawarin da Kwankwasiyya ta yi, saboda haka ba a dauki lokaci ba sai aka gabatar da bukatar sake duba dokar da majalisar dokokin lokacin Ganduje ta zartar wadda aka yi amfani da ita wajen cire Sanusi II.

Bayan shigar da Muhammadu Sanusi II gidan Dabo cikin dare, sai Sarki Aminu ya dawo daga tafiyarsa washegari inda ya wuce karamar fadar da ke gidan Sarki na Nasarawa, wanda tun daga wancan lokacin a karon farko sarakuna biyu ke gabatar da mulkin masarautar ta Kano daga wurare daban-daban.

Babban kalubalen da Sarkin Sanusi ke fuskanta shi ne, rashin samun goyon bayan gwamnatin tarayya, musamman ganin jam’iyyar APC ke mulki, wanda shi kuma Sarki Sanusi jama’a sun gamsu da yadda ya taimaka wajen kayar da jam’iyyar a Kano, saboda alkawarin da Kwankwasawa suka yi masa na dawo da shi kan kargar sarautar Kano.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Sarki Aminu wanda ke samun goyon bayan gwamnatin tarayya da kuma umarnin wasu kotuna guda biyu da hukuncinsu ya tabbatar da shi a matsayin halastaccen sarki, ya kasance yana ci gaba da aiwatar da harkokin mulki daga waccan karamar fadar, tare da fuskantar kalubale daga bangaren Gwamnatin Jihar Kano, wadda har majalisa aka kai bukatar rushe katangar gidan sarkin na Nasarawa da sunan za a gyara gidan.

Sakamakon wannan ne ya sa tsohon gwamnan Kano kuma shugaban jam’iyyar APC na kasa ake ganin yana cikin wadanda suka hana Sarki Sanusi II rawar gaban hantsi, sannan kuma ya toshe duk wata kofa da gwamnatin Kano ka iya samu wajen karfafa mulkin Sarkin Sanusi, sannan akwai kotuna guda biyu duk na gwamnatin tarayya ne wadada hukuncinsu ya bai wa Sarki Aminu gaskiya a shari’un da ke gabansu, saboda haka hukuncin da ake sauraro yanzu shi ne ka iya nuna makomar Sarki Sanusi II da kuma shi kansa Sarki Aminu.

Sai dai kuma daga irin abubuwan da ake gani a duk lokacin da wani daga cikin sarakunan biyu ya fito cikin al’umma, ana iya fahimtar wanda talakawa suka fi sha’awa, musamman duba da dawowar Sarki Sanusi daga kasar Ingila, lokacin ya je kare digirin-digirgir dinsa, yayin da shi kuma sarki Aminu ya halarci taro da aka saba gudanarwa duk shekara a masallachi Marigayi Khalifa Isyaka Rabi’u.

Saboda haka batun da ake na cewa Dakta Ganduje na shirya wata kulalliya domin tabbatar da sallamar Sarki Sanusi II ba wani sabon abu ba ne, domin yana daga cikin alkawuran da gwamnatin Kano ta yanzu ke kansu na yin duk mai yiwuwa wajen rushe duk wani tsari na Ganduje, sannan kuma kusancinsa da shugaban kasa, musamman kasancewarsa shugaban jam’iyyar da Bola Tinubu ya ci zabe karkashin tutarta.

Muhimmancin Jihar Kano a wurin gwamnatin tarayya ya sa wasu ke ganin su Ganduje za su ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen ganin sun hana Sarki Sanusi zama a karaga.

Yanzu haka akwai kishin-kishin cewa, Ganduje ya tattaro mukarabbansa ciki har da ‘yan kasuwa da manyan dattawan jihar domin neman Shugaba Bola Tinubu ya sa baki Sarki Sanusi da Sarki Aminu kowa ya hakura domin samun maslaha.

Sai dai har yanzu abin na nan lullube a cikin duhu wanda lokaci ne kadai iya tabbatarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aminu Ado BayerokanoSakarunaSanusi IISarauta
ShareTweetSendShare
Previous Post

Maulidi: Fityanul Islam Ta Jajanta Wa Al’ummar Borno Kan Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Next Post

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

Related

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

8 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

10 hours ago
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Labarai

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

11 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

13 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar HaÉ—aka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar HaÉ—aka

13 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

16 hours ago
Next Post
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.