• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Sanatan APC Ya Nemi Monguno Ya Yi Murabus

bySadiq
3 years ago
Monguno

Sanata mai wakiltar Neja ta Gabas, Sani Musa, ya ce Babagana Monguno, mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), ya yi murabus saboda tabarbarewar tsaro a kasar.

Musa ya soki hukumar NSA da cewa ba ita ce ta fara sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari barazanar da ‘yan ta’adda ke yi na sace shi ba.

  • ‘Yan Bindiga Na Kwararowa Jihata – Gwamnan Nasarawa
  • ‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

Sanatan yabyi magana ne a ranar Lahadi a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

A karshen makon da ya gabata ne wani faifan bidiyo da ‘yan ta’adda suka saki, suka yi barazanar sace Buhari da gwamnan jihar Kaduna, Nasir el-Rufai, ya karade shafukan sada zumunta.

Da yake magana kan lamarin a ranar Laraba, El-Rufai ya ce shugaba Buhari bai san da barazanar sai da ya sanar da shi da kansa.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Musa, wani jigo a jam’iyyar APC, ya ce “bisa dukkan alamu” cewa shugaban kasa ba shi da masaniyar lamarin.

“Idan har gaskiya ne, idan aka yi la’akari da maganar gwamna El-Rufai na cewa shugaban kasa bai sani ba, wannan lamari kadai ya isa a kori NSA.

“Ana kashe mutane a kasa, kuma za ka gaya min cewa a matsayina na shugaban kasa don tsara yadda ya kamata tsaronmu ya kasance, ba ka da masaniya kan haka kuma ba za a iya sanar da shugaban kasa ba. Ya kamata a sallami NSA.”

Da yake karin haske kan matsalar rashin tsaro, Sanatan Neja, ya ce da ya yi murabus idan shi ne NSA na shugaban kasa, inda ya kara da cewa jami’an tsaro a ko da yaushe sun kasa yin aiki da rahotannin sirri.

“Dole ne mu kira. Da ni ne mai ba kasa shawara kan harkokin tsaro a kasar nan da zan mika takardar murabus dina saboda na gaza. Ba ku jira sai lokacin da aka kawo muku hari sannan za ku yi aiki ba.

“Wadannan bayanan sirrin da ake rabawa bayanai ne da aka ba ku a wani mataki da masu laifin ba su cumma manufarsu da shirinsu ba kuma za ku kawar da su.

“Don haka a gare ni, na yi imani cewa muna bukatar mu sake tsara dabarunmu duba da yawan al’umma. Idan ka je jihar Neja, yau za ka ga ‘yan gudun hijira da dama, mutane sun bar garuruwansu.”

A baya-bayan nan ne mai bai wa shugaban kasa kan sha’anin tsaro, ya ce ‘yan Nijeriya sun gaji da matsalar tsaro a kasar, inda ta kara da cewa ‘yan kasar na kokarin neman taimakon kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version