ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Sanatan APC Ya Nemi Monguno Ya Yi Murabus

by Sadiq
4 years ago
Monguno

Sanata mai wakiltar Neja ta Gabas, Sani Musa, ya ce Babagana Monguno, mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), ya yi murabus saboda tabarbarewar tsaro a kasar.

Musa ya soki hukumar NSA da cewa ba ita ce ta fara sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari barazanar da ‘yan ta’adda ke yi na sace shi ba.

  • ‘Yan Bindiga Na Kwararowa Jihata – Gwamnan Nasarawa
  • ‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

Sanatan yabyi magana ne a ranar Lahadi a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

ADVERTISEMENT

A karshen makon da ya gabata ne wani faifan bidiyo da ‘yan ta’adda suka saki, suka yi barazanar sace Buhari da gwamnan jihar Kaduna, Nasir el-Rufai, ya karade shafukan sada zumunta.

Da yake magana kan lamarin a ranar Laraba, El-Rufai ya ce shugaba Buhari bai san da barazanar sai da ya sanar da shi da kansa.

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

Musa, wani jigo a jam’iyyar APC, ya ce “bisa dukkan alamu” cewa shugaban kasa ba shi da masaniyar lamarin.

“Idan har gaskiya ne, idan aka yi la’akari da maganar gwamna El-Rufai na cewa shugaban kasa bai sani ba, wannan lamari kadai ya isa a kori NSA.

“Ana kashe mutane a kasa, kuma za ka gaya min cewa a matsayina na shugaban kasa don tsara yadda ya kamata tsaronmu ya kasance, ba ka da masaniya kan haka kuma ba za a iya sanar da shugaban kasa ba. Ya kamata a sallami NSA.”

Da yake karin haske kan matsalar rashin tsaro, Sanatan Neja, ya ce da ya yi murabus idan shi ne NSA na shugaban kasa, inda ya kara da cewa jami’an tsaro a ko da yaushe sun kasa yin aiki da rahotannin sirri.

“Dole ne mu kira. Da ni ne mai ba kasa shawara kan harkokin tsaro a kasar nan da zan mika takardar murabus dina saboda na gaza. Ba ku jira sai lokacin da aka kawo muku hari sannan za ku yi aiki ba.

“Wadannan bayanan sirrin da ake rabawa bayanai ne da aka ba ku a wani mataki da masu laifin ba su cumma manufarsu da shirinsu ba kuma za ku kawar da su.

“Don haka a gare ni, na yi imani cewa muna bukatar mu sake tsara dabarunmu duba da yawan al’umma. Idan ka je jihar Neja, yau za ka ga ‘yan gudun hijira da dama, mutane sun bar garuruwansu.”

A baya-bayan nan ne mai bai wa shugaban kasa kan sha’anin tsaro, ya ce ‘yan Nijeriya sun gaji da matsalar tsaro a kasar, inda ta kara da cewa ‘yan kasar na kokarin neman taimakon kai.

MASU ALAKA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya
Labarai

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Next Post
DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.