ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Sanatan APC Ya Nemi Monguno Ya Yi Murabus

by Sadiq
4 years ago
Monguno

Sanata mai wakiltar Neja ta Gabas, Sani Musa, ya ce Babagana Monguno, mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), ya yi murabus saboda tabarbarewar tsaro a kasar.

Musa ya soki hukumar NSA da cewa ba ita ce ta fara sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari barazanar da ‘yan ta’adda ke yi na sace shi ba.

  • ‘Yan Bindiga Na Kwararowa Jihata – Gwamnan Nasarawa
  • ‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

Sanatan yabyi magana ne a ranar Lahadi a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

ADVERTISEMENT

A karshen makon da ya gabata ne wani faifan bidiyo da ‘yan ta’adda suka saki, suka yi barazanar sace Buhari da gwamnan jihar Kaduna, Nasir el-Rufai, ya karade shafukan sada zumunta.

Da yake magana kan lamarin a ranar Laraba, El-Rufai ya ce shugaba Buhari bai san da barazanar sai da ya sanar da shi da kansa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Musa, wani jigo a jam’iyyar APC, ya ce “bisa dukkan alamu” cewa shugaban kasa ba shi da masaniyar lamarin.

“Idan har gaskiya ne, idan aka yi la’akari da maganar gwamna El-Rufai na cewa shugaban kasa bai sani ba, wannan lamari kadai ya isa a kori NSA.

“Ana kashe mutane a kasa, kuma za ka gaya min cewa a matsayina na shugaban kasa don tsara yadda ya kamata tsaronmu ya kasance, ba ka da masaniya kan haka kuma ba za a iya sanar da shugaban kasa ba. Ya kamata a sallami NSA.”

Da yake karin haske kan matsalar rashin tsaro, Sanatan Neja, ya ce da ya yi murabus idan shi ne NSA na shugaban kasa, inda ya kara da cewa jami’an tsaro a ko da yaushe sun kasa yin aiki da rahotannin sirri.

“Dole ne mu kira. Da ni ne mai ba kasa shawara kan harkokin tsaro a kasar nan da zan mika takardar murabus dina saboda na gaza. Ba ku jira sai lokacin da aka kawo muku hari sannan za ku yi aiki ba.

“Wadannan bayanan sirrin da ake rabawa bayanai ne da aka ba ku a wani mataki da masu laifin ba su cumma manufarsu da shirinsu ba kuma za ku kawar da su.

“Don haka a gare ni, na yi imani cewa muna bukatar mu sake tsara dabarunmu duba da yawan al’umma. Idan ka je jihar Neja, yau za ka ga ‘yan gudun hijira da dama, mutane sun bar garuruwansu.”

A baya-bayan nan ne mai bai wa shugaban kasa kan sha’anin tsaro, ya ce ‘yan Nijeriya sun gaji da matsalar tsaro a kasar, inda ta kara da cewa ‘yan kasar na kokarin neman taimakon kai.

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.