• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Tana Raba “Sirrin” Ci Gabanta Ga Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Kasar Sin Tana Raba “Sirrin” Ci Gabanta Ga Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 1 ga watan Oktoba mai zuwa ce ranar cika shekaru 75 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin. Idan muka waiwayi tarihin ci gaban kasar, za mu ga cewa, ta yi aiki tukuru don kara karfinta, duk da cewa tana fama da talauci, da rauni a lokacin kafuwarta, inda ta kafa harsashin masana’antu ta hanyar dogaro da kai, da samun nasarar shiga kasuwannin kasa da kasa ta hanyar hadin gwiwa da bude kofa, sannan ta ci gaba da inganta shirinta na raya kasa, kuma sannu a hankali ta zama kasa mafi karfin tattalin arziki ta biyu a duniya, bisa la’akari da matsayin GDP. Bayan an takaita tarihin kasar, matakan da ta dauka a kokarin raya kanta kamar ba su da sarkakiya, sai dai kalilan kasashe ne za su iya kiyaye irin wannan ci gaba cikin sauri na dogon lokaci da kasar Sin ta samu. To ko mene ne sirrin kasar Sin a fannin raya kasa?

 

Idan ka tambayi dan kasar Sin yadda rayuwarsa ta canza a cikin shekaru ashirin da suka gabata ko ma fiye da haka, tabbas zai ambaci abubuwa da yawa: samun karin kudin shiga, da karin abinci masu gina jiki. Kana an samu zama cikin sabbin gidaje masu inganci, yayin da harkar sayayya ta zama mai sauki da ban sha’awa, da dai sauransu, wato dukkan bangarorin suna inganta. Irin wannan ci gaba na hakika da aka samu a cikin rayuwar jama’a, sakamakon ci gaban kasar Sin ne, kuma dalilinsa ne.

  • Ambaliya: Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Bai Wa Maiduguri Tallafin Miliyan 20
  • Aikin Matatar Mai Na Ya Hana Ni Sayen Arsenal A 2020 – Dangote

Masu mulkin kasar Sin suna da wani muhimmin tunanin da ake kira “Mai da jama’a a gaban komai.” A nasu ra’ayin, kasa tana bauta wa al’umma, kuma dalilin da ya sa ake neman ci gaban kasa shi ne don baiwa al’umma damar rayuwa mai inganci. Wannan ra’ayi ne da ya sa al’ummar kasar Sin kokarin hadin kai da juna, ta yadda siyasar kasar ta tabbata. Mutane sun yi imanin cewa rayuwarsu za ta kara kyau a nan gaba, kuma kokarin aiki zai haifar da sakamako mai gamsarwa. A sakamakon haka, ana bin dokoki, ana aiwatar da manufofi, ana kokarin cimma burikan da aka sanya daya bayan daya.

 

Labarai Masu Nasaba

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Da an ji batun “Mai da jama’a a gaban komai”, za a ga tamkar babbar magana ce, amma ana iya ganin misalan aiwatar da hakan a ko ina a kasar Sin: A kasuwannin birnin Beijing, sau da yawa na sayi kayayyakin nau’in “kau da talauci da taimakon manoma”(gwamnati na taimakawa yankunan da suke da koma baya ta fuskar tattalin arziki wajen bunkasa sana’o’i. Inda ta hanyar kera wasu kayayyaki na musamman, ana raya masana’antun da za su iya samar da kudin shiga, don tabbatar da ci gaban tattalin arziki da karin ayyukan yi). A gundumar Chun’an da ke lardin Zhejiang na kasar Sin, na ga yadda aka tsara kauyuka bisa yanayin albarkatunsu, don raya wasu sana’o’i daban-daban, kamar kera magungunan gargajiya, da bunkasa ayyukan gona ba tare da gurbata muhallin halittu ba, da kiwon kifi, da yawon bude ido, da dai sauransu, ta yadda aka samar da isassun damammaki ga mazauna kauyukan domin su wadata. Kana a tashar jiragen ruwa ta garin Ningbo, dake gabashin kasar Sin, na ga sabbin fasahohi da ke baiwa ma’aikata damar zama a ofisoshi, da sarrafa injuna masu kwashe kwantenoni ta na’urorin da ake sarrafawa daga nesa, ta yadda ba za su ci gaba da shan wahalar aiki a karkashin zafin rana ba. Ban da haka, ana ci gaba da kokarin gina layukan dogo masu inganci a tsakanin biranen kasar Sin, lamarin da ke baiwa jama’a sauki wajen yin balaguro a kasar…

 

A halin yanzu, yayin da hadin gwiwar Sin da Afirka ke ci gaba da zurfafa, ana tabbatar da manufar “Mai da jama’a a gaban komai” a dimbin ayyukan da suke amfanar da jama’ar Sin da Afirka. Misali, a birnin Lagos na Najeriya, layin dogo na Blue Line da wani kamfanin kasar Sin ya gina, ba kawai yana saukaka tafiye-tafiyen jama’a ba, har ma ya samar da taimako a fannin rage cunkoso a cikin gari. Yana kuma rage fitar da gurbataccen hayaki, da samar da ayyukan yi ga daruruwan mutane.

 

A kauyuka da dama na Najeriya kuwa, kamfanonin kasar Sin sun samar da tashoshin wayar salula masu amfani da makamashin hasken rana, lamarin da ya bai wa fiye da mutane miliyan 7 dake yankunan karkara damar yin amfani da yanar gizo ko intanet. Kana a kasar Kenya, nau’in shinkafa da kwararrun masanan ilimin aikin gona na kasar Sin suka samar, ya sa yawan shinkafar da ake samu ta karu matuka, a lokacin da ake gwajin nomanta, wanda hakan ya baiwa kasar damar samun isashen abinci bisa dogaro da kai. Ban da haka, cibiyoyin koyar da ilimin sana’a na “Luban Workshop” guda 17 da kasar Sin ta kafa a sassan kasashen Afirka, sun samar da fasahohin sana’o’i da guraben aikin yi ga dubun dubatar matasan Afirka…

 

Idan manufar “Mai da jama’a a gaban komai” ita ce “Sirrin” ci gaba mai dorewa na kasar Sin, to, Sin ta raba wa kasashen Afirka wannan muhimmin sirrinta. A gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a baya-bayan nan a birnin Beijing na kasar Sin, kasar ta ba da shawarar yin aiki tare da kasashen Afirka wajen zamanintar da kansu, da mai da kare moriyar jama’a gaban duk wani aiki na daban. Ta haka, babu shakka, al’ummar kasashen Afirka za su samu karin fa’ida, wadda kuma za ta zama tushen ci gaban tattalin arzikin Afirka. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Ta’addanci A Zamfara: Matawalle Ya Ƙalubalanci Gwamna Dauda Su Yi Rantsuwa Da Alƙur’ani

Next Post

Kasar Sin Ta Lashi Takobin Karfafa Hidimomin Kula Da Tsoffi

Related

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

3 days ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

7 days ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

1 week ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

2 weeks ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

2 weeks ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

2 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Ta Lashi Takobin Karfafa Hidimomin Kula Da Tsoffi

Kasar Sin Ta Lashi Takobin Karfafa Hidimomin Kula Da Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

August 15, 2025
Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

August 15, 2025
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

August 15, 2025
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

August 15, 2025
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

August 15, 2025
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

August 15, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

August 15, 2025
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.