ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Tana Raba “Sirrin” Ci Gabanta Ga Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Ranar 1 ga watan Oktoba mai zuwa ce ranar cika shekaru 75 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin. Idan muka waiwayi tarihin ci gaban kasar, za mu ga cewa, ta yi aiki tukuru don kara karfinta, duk da cewa tana fama da talauci, da rauni a lokacin kafuwarta, inda ta kafa harsashin masana’antu ta hanyar dogaro da kai, da samun nasarar shiga kasuwannin kasa da kasa ta hanyar hadin gwiwa da bude kofa, sannan ta ci gaba da inganta shirinta na raya kasa, kuma sannu a hankali ta zama kasa mafi karfin tattalin arziki ta biyu a duniya, bisa la’akari da matsayin GDP. Bayan an takaita tarihin kasar, matakan da ta dauka a kokarin raya kanta kamar ba su da sarkakiya, sai dai kalilan kasashe ne za su iya kiyaye irin wannan ci gaba cikin sauri na dogon lokaci da kasar Sin ta samu. To ko mene ne sirrin kasar Sin a fannin raya kasa?

 

Idan ka tambayi dan kasar Sin yadda rayuwarsa ta canza a cikin shekaru ashirin da suka gabata ko ma fiye da haka, tabbas zai ambaci abubuwa da yawa: samun karin kudin shiga, da karin abinci masu gina jiki. Kana an samu zama cikin sabbin gidaje masu inganci, yayin da harkar sayayya ta zama mai sauki da ban sha’awa, da dai sauransu, wato dukkan bangarorin suna inganta. Irin wannan ci gaba na hakika da aka samu a cikin rayuwar jama’a, sakamakon ci gaban kasar Sin ne, kuma dalilinsa ne.

ADVERTISEMENT
  • Ambaliya: Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Bai Wa Maiduguri Tallafin Miliyan 20
  • Aikin Matatar Mai Na Ya Hana Ni Sayen Arsenal A 2020 – Dangote

Masu mulkin kasar Sin suna da wani muhimmin tunanin da ake kira “Mai da jama’a a gaban komai.” A nasu ra’ayin, kasa tana bauta wa al’umma, kuma dalilin da ya sa ake neman ci gaban kasa shi ne don baiwa al’umma damar rayuwa mai inganci. Wannan ra’ayi ne da ya sa al’ummar kasar Sin kokarin hadin kai da juna, ta yadda siyasar kasar ta tabbata. Mutane sun yi imanin cewa rayuwarsu za ta kara kyau a nan gaba, kuma kokarin aiki zai haifar da sakamako mai gamsarwa. A sakamakon haka, ana bin dokoki, ana aiwatar da manufofi, ana kokarin cimma burikan da aka sanya daya bayan daya.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Da an ji batun “Mai da jama’a a gaban komai”, za a ga tamkar babbar magana ce, amma ana iya ganin misalan aiwatar da hakan a ko ina a kasar Sin: A kasuwannin birnin Beijing, sau da yawa na sayi kayayyakin nau’in “kau da talauci da taimakon manoma”(gwamnati na taimakawa yankunan da suke da koma baya ta fuskar tattalin arziki wajen bunkasa sana’o’i. Inda ta hanyar kera wasu kayayyaki na musamman, ana raya masana’antun da za su iya samar da kudin shiga, don tabbatar da ci gaban tattalin arziki da karin ayyukan yi). A gundumar Chun’an da ke lardin Zhejiang na kasar Sin, na ga yadda aka tsara kauyuka bisa yanayin albarkatunsu, don raya wasu sana’o’i daban-daban, kamar kera magungunan gargajiya, da bunkasa ayyukan gona ba tare da gurbata muhallin halittu ba, da kiwon kifi, da yawon bude ido, da dai sauransu, ta yadda aka samar da isassun damammaki ga mazauna kauyukan domin su wadata. Kana a tashar jiragen ruwa ta garin Ningbo, dake gabashin kasar Sin, na ga sabbin fasahohi da ke baiwa ma’aikata damar zama a ofisoshi, da sarrafa injuna masu kwashe kwantenoni ta na’urorin da ake sarrafawa daga nesa, ta yadda ba za su ci gaba da shan wahalar aiki a karkashin zafin rana ba. Ban da haka, ana ci gaba da kokarin gina layukan dogo masu inganci a tsakanin biranen kasar Sin, lamarin da ke baiwa jama’a sauki wajen yin balaguro a kasar…

 

A halin yanzu, yayin da hadin gwiwar Sin da Afirka ke ci gaba da zurfafa, ana tabbatar da manufar “Mai da jama’a a gaban komai” a dimbin ayyukan da suke amfanar da jama’ar Sin da Afirka. Misali, a birnin Lagos na Najeriya, layin dogo na Blue Line da wani kamfanin kasar Sin ya gina, ba kawai yana saukaka tafiye-tafiyen jama’a ba, har ma ya samar da taimako a fannin rage cunkoso a cikin gari. Yana kuma rage fitar da gurbataccen hayaki, da samar da ayyukan yi ga daruruwan mutane.

 

A kauyuka da dama na Najeriya kuwa, kamfanonin kasar Sin sun samar da tashoshin wayar salula masu amfani da makamashin hasken rana, lamarin da ya bai wa fiye da mutane miliyan 7 dake yankunan karkara damar yin amfani da yanar gizo ko intanet. Kana a kasar Kenya, nau’in shinkafa da kwararrun masanan ilimin aikin gona na kasar Sin suka samar, ya sa yawan shinkafar da ake samu ta karu matuka, a lokacin da ake gwajin nomanta, wanda hakan ya baiwa kasar damar samun isashen abinci bisa dogaro da kai. Ban da haka, cibiyoyin koyar da ilimin sana’a na “Luban Workshop” guda 17 da kasar Sin ta kafa a sassan kasashen Afirka, sun samar da fasahohin sana’o’i da guraben aikin yi ga dubun dubatar matasan Afirka…

 

Idan manufar “Mai da jama’a a gaban komai” ita ce “Sirrin” ci gaba mai dorewa na kasar Sin, to, Sin ta raba wa kasashen Afirka wannan muhimmin sirrinta. A gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a baya-bayan nan a birnin Beijing na kasar Sin, kasar ta ba da shawarar yin aiki tare da kasashen Afirka wajen zamanintar da kansu, da mai da kare moriyar jama’a gaban duk wani aiki na daban. Ta haka, babu shakka, al’ummar kasashen Afirka za su samu karin fa’ida, wadda kuma za ta zama tushen ci gaban tattalin arzikin Afirka. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Lashi Takobin Karfafa Hidimomin Kula Da Tsoffi

Kasar Sin Ta Lashi Takobin Karfafa Hidimomin Kula Da Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.