Ma’aikatar kula da harkokin al’umma ta kasar Sin ta lashi takobin karfafa hidimomin kula da tsoffi a kasar, domin al’ummar kasar da suka manyanta.
Ministan ma’aikatar Lu Zhiyuan, ya bayyana yayin wani taron manema labarai a jiya Litinin cewa, ma’aikatar ta kafa wani tsari mai matakai 3 na bayar da hidimomin kula da tsoffi da zai hada gundumomi da garuruwa da kauyuka.
- Zargin Ta’addanci A Zamfara: Matawalle Ya Ƙalubalanci Gwamna Dauda Su Yi Rantsuwa Da Alƙur’ani
- Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya
A cewar Lu Zhiyuan, domin amfana da tsarin samar da hidimomin, za a karfafa tare da kyautata cibiyoyin kula da tsoffi dake unguwanni. Ya ce wadannan cibiyoyin za su samar da taimakon abinci da na kiwon lafiya da na bukatun gaggawa a matsayin wani bangare na kula da tsoffi a gidajensu, wanda zai karfafa tubalin wannan bangare.
Har ila yau, domin karfafa bangaren kula da tsoffin, ministan ya ce za a yi kokarin tallafawa tare da samar da kwararru da kayayyakin kula da tsoffi da fadada amfana da hidimomin da kuma kara raya tattalin arzkin bangaren hidimtawa tsoffi. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp