• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yara 2,300 Da Mata 145 Ke Mutuwa Kul-lum A Nijeriya — NPHCDA

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Yara 2,300 Da Mata 145 Ke Mutuwa Kul-lum A Nijeriya — NPHCDA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban daraktan hukumar kula da lafiya a matakin farko ta kasa (NPHCDA), Dakta Muyi Aina, ya ce, har yanzu mata da dama na rasa rayukansu a Nijeriya sakamakon juna biyu da kuma wurin haihuwa, sannan kuma jarirai da dama ba su samun zarafin kai wa shekaru biyar a duniya sakamakon cuttukan da aka kasa shawo kansu.

 

Aina ya shaida hakan ne a ranar Litinin a Abuja a wajen taron wayar da kai kan rigakafi da batutuwan kula da lafiyar mata da yara wanda gidauniyar Sultan ta fadi tashin wanzar da zaman lafiya (SFPD) da hadin gwiwar NPHCDA suka shirya wa shugabannin addini daga yankin arewacin Nijeriya.

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Manoma 6 Da Aka Sace A Katsina
  • EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Taraba Ishaku Kan Zargin Badaƙalar 27bn

Shugaba NPHCDA ya kuma kara da cewa Nijeriya ta samu kesa-kesai 70 na kara-min cutar foliyo Type 2 daga kananan hukumomi 46 a jihohin arewacin Nijeriya 14, inda ya ce an samu wannan ne sakamakon rashin yin rigakafi a kai a kai, yayin da wasu kuma ke kin amsar rigakafin foliyo a lokacin da ake gangamin wayar musu da kai.

“A kowace rana, Nijeriya tana rasa sama da yara ‘yan kasa da shekara 5 guda 2,300 da kuma rasa iyaye mata 145 masu dauke da juna biyu a wajen haihuwa. Dukkanin wadannan mace-macen na faruwa ne a yankin arewaci.

Labarai Masu Nasaba

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

“Dole ne a canza wannan matsalar. Dole mu tabbatar kowace mace na sun zuwa awo da kuma kulawar da suka dace, kowace mace mai juna biyu ta haihu a han-nun kwararrun unguwar zoma, kuma kowani yaro ya samu damar kammala am-sar rigakafin kamar yadda yake kunshe cikin tsarin kasa, kuma a tabbatar sun samu rigakafi a kowani lokaci a gidajensu. In muka hada hannu za mu cimma na-sarar zuwa matakin da babu wani yaro da za a bar shi ba tare da ya samu rigakafi ba.”

Aina ya bukaci shugabannin addini da su kara jan damara da himma domin ganin an samu inganta kiwon lafiyan jama’a. Ya ce, akwai bukatar a cire dabi’ar wariya wajen bayar da kiwon lafiya ga mutane tare da tabbatar da kowa na samun ku-lawar kiwon lafiya yadda ya dace.

Daga bisani ya jinjina wa Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, da babban Rabaran, Daniel Okoh bisa gayyato shugabannin addinai da sarakuna da suka yi domin samun wannan horon na musamman kan yadda za a kara wayar da kan jama’a game da muhimmancin rigakafi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cibiyoyin kiwon lafiyaMutuwar kananan yara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai: Tinubu Ya Mayar Da Hankali Kan Haɓaka Tattalin Arziƙin Nijeriya – Minista

Next Post

An Fara Tantance Mutane 7,000 da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Limanti

Related

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote
Manyan Labarai

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

1 minute ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

60 minutes ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

1 hour ago
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
Labarai

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

2 hours ago
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
Labarai

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

3 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

5 hours ago
Next Post
An Fara Tantance Mutane 7,000 da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Limanti

An Fara Tantance Mutane 7,000 da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Limanti

LABARAI MASU NASABA

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote

July 11, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.