• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 10 Da Jawabin Tinubu Na Ranar ‘Yancin Kai Ya Kunsa 

by Khalid Idris Doya, Sulaiman and CGTN Hausa
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Muhimman Abubuwa 10 Da Jawabin Tinubu Na Ranar ‘Yancin Kai Ya Kunsa 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da jawabi ga al’umman kasa cikin bukukuwan ranar samun ‘yancin kai karo na 64, inda ya ce, sabbin manufofi da tsare-tsarensa sun fara ba da sakamakon da ake nema. 

 

Ya kuma sanar da aniyar gwamnatinsa na shigo da matasa a dama da su a cikin gwamnatinsa da ba su damarmaki ta hanyar gudanar da babban taron matasa na kasa na kwanaki 30.

 

Ga muhimman abubuwa 10 da jawabin Tinubu ya kunsa kamar haka:

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Amincewa Da Matsalolin Da Suke Jibge: Tinubu ya ce, yana sane da irin yadda ‘yan Nijeriya da dama ke shan wahalar tsadar rayuwa, tsadar kayan abinci da matsalar rashin ayyukan yi. Ya ba da tabbacin shawo kansu.

 

Jajircewa: Tinubu ya yi tsokaci kan ci gaban da Nijeriya ta samu tun bayan samun ‘yancin kai, ya lura kan cewa kasar ta samu tsayuwa da kanta duk da rikice-rikice irinsu yakin basasa, da dai sauransu.

 

Yunkurin Samar Da Tsaro: Ya bayyana muhimman nasarorin da ake samu wajen yaki da ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane, da sauran nau’ikan ayyukan ta’addanci. Ya samar da kashe sama da kwamandoji 30 na Boko Haram da sauran kungiyoyin masu dauke da bindigogi.

 

Farfado Da Tattalin Arziki: Tinubu ya jaddada wajibcin yin garambawul ga tsare-tsaren tattalin arzikin domin shawo kan matsalolin da suke jibge a sha’anin kudi. Ya ce wannan yunkurin ya kai ga janyo dala biliyan 30 na zuba hannun jarin kasashen waje da kuma inganta hada-hadar kudade.

 

Yunkurin Rage Matsin Rayuwa: Tinubu ya amince da irin wahalar da jama’a ke sha da matsin rayuwa, musamman kan tsadar farashin kayayyakin abinci, har ma ya ce, “Babban abun da ya fi damun mutanenmu a yau shi ne tsadar rayuwa, musamman kan kayayyakin abinci. Wannan lamarin ya shafi mutane da dama a fadin duniya, inda farashin da tsadar rayuwa ke ci gaba da faruwa a fadin duniya. “Muna sa ran ganin an samu karin amfanin da ake fitarwa da kuma raguwar tsadar kayan abinci.

 

Samar Da Ayyuka Ga Matasa: Shugaban ya sanar da shirin gudanar da babban taron matasa na kasa da kuma wasu shirye-shiryen da aka ware su kai tsaye ga matasa ciki kuwa har da shirin 3MTT na baje fasaha da kuma asusun rancen ilimi na Nijeriya. “Wannan babban taron zai taimaki matasanmu su samu shiga a dama da su a cikin gudanar da mulki.”

 

‘Yancin Cin Kashin Kan Kananan Hukumomi A Bangaren Kudade: Tinubu ya jaddada aniyarsa na aiwatar da hukuncin umarnin kotun koli na bai wa kananan hukumomi kason kudadensu kai tsaye.

 

Shirye-shirye Kan Makamashi Da Sufuri: Ya sanar da shirinsa na fadada rungumar motocin da ke amfani da iskar gas. Ya ce, “Yunkurinmu na kyautata makamashi na tafi kan turba. Muna fadada shirinmu na amfani da motoci masu amfani da iskar gas a bangaren sufuri. Gwamnatin tarayya a shirye take ta mara wa jihohi 36 ciki har da Babban Birnin Tarayya baya da su mallaki motocin domin saukaka wa jama’a sufuri.”

 

Rage Radadin Annoba Da Matakan Kariya: Shugaban kasa ya kuma yi magana kan yunkurin gwamanti na tunkarar ibtila. Ya ce, “Gwamnatinmu na tunkarar ibtila da aka samu baya-bayan nan, musamman ma na ambaliyar ruwa a wasu sassan kasa. Bayan ziyarar da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya kai Maiduguri, Ni ma da kaina na je na ziyarci garin domin tabbatar wa jama’anmu cewa wannan gwamnatin tarayyar a kowani lokaci tana tare da mutanenta a kowani lokaci. A taron karshe na majalisar koli ta kasa, mun amince da samar da asusun kula da ibtila’i da samar da yanayin da masu kamfanoni da daidaiku za su taimaka mana wajen tunkarar matsaloli cikin gaggawa.

 

Kyakkyawar Fata Ga Ci Gaba: Ya karkare jawabinsa da karfafan ‘yan Nijeriya da cewa, ka da su yanke kauna, su ci gaba da jajircewa da yin aikin hadin gwiwa domin ci gaba da kuma rayuwar gobe. Ya kuma nanata aniyar gwamnatinsa na kara shigo da kowani bangare da samar da ci gaba mai dorewa da kuma hadin kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yancin KaiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Next Post

Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW)

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

6 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

19 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

1 day ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

1 day ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

2 days ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
Next Post
Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW)

Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.