ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Kwankwaso Da Obi, Waye Babba A Siyasa?

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Kwankwaso

A siyasance, kowa yana so a ce shi ne babba, inda jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabi’u Kwankwaso, ya fito fili ya nuna cewa shi ne babba a tsakaninsa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Mista Peter Obi.

Wannan takaddama ta kunno kai ne tun lokacin da wasu masu ruwa da tsaki suka bukaci Kwankwaso ya amince da shirinsu na zama a abokin takarar Obi a zaben shugaban kasa a 2027.

  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100
  • Matasa 3 Sun Shiga Hannu Kan Kashe Wani Mutum Don Mallakar Filinsa A Kano

Tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda kuma shi ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya ce yana jira ya ga ka’idojin da za a yi amfani da su wajen gudanar da irin wannan tsarin, duba da irin iliminsa da siyasa a kan Obi.

ADVERTISEMENT

A wani faifan bidiyo da ya yi ta yawo a kafafen sada zumunta a ranar Asabar, an ga Kwankwaso na bayyana cewa, “Na fi Peter Obi girma a siyasance. Ni babban yayansa ne. Ina da kwarewa fiye da shi. Na yi kokari fiye da shi lokacin da nake gwamnan jihata.

“Ba ni da matsala wajen zama mataimakin takarar Peter Obi, amma sai dai idan an cika wasu sharudda,” in ji shi, yana mai jaddada cewa duk wani kawancen da za a iya kullawa dole ne a gina shi bisa amana.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Ya kara da cewa, “A shirye muke mu tattaunawa, muddin aka amince da sharuddanmu,” in ji shi, wanda ke nuna cewa shi da Obi a shirye suke su kulla kawancen siyasa da shugabancin jam’iyyar LP a gabanin zaben 2027.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Obi ne ya zo na uku a zaben da ya gabata da kuri’u 6,101,533, yayin da Kwankwaso ya taka rawar gani a jiharsa ta Kano, ya samu kuri’u 1,496,687 a kananan hukumomi 38 daga cikin 44 na jihar.

Kwankwaso ya kuma kasance mai sukar gwamnatin Shugaban kasa Bola Tinubu, musamman game da rabon kayan tallafin shinkafa a Jihar Kano. Ya zargi gwamnatin tarayya da kin bai wa gwamnatin jihar tallafin tare da mika wa ga ‘yan jam’iyyar adawa ta APC a jihar.

“Abun takaicin ne yadda gwamnatin tarayya ta raba tallafin shinkafa ga jihohi 35 a hannun gwamnoninsu, in ban da Jihar Kano wanda ak mika kason ga jiga-jigan APC. Wannan babban cin fuska ne ga dimokuradiyyar da kuma tsarin mulkinmu,” in ji Kwankwaso a wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Tuwita.

Sai dai kuma, tsohon mai magana da yawun tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad ya mayar wa da Kwankwaso martini, inda ya bayyana cewa Obi ne babba a siyasance fiye da Kwankwaso.

Ahmad, a cikin wani rubutu a shafinsa na Tuwita, ya ce duk da cewa ya kasance yana girmama Kwankwaso a matsayinsa na dan siyasa mai ci gaba, ba zai iya yin bara’a da furucin nasa ba.

Ya rubuta cewa, “Duk da cewa ban taba zama mai biyayya ga Kwankwasiyya ba, amma a ko da yaushe ina girmama Sanata Rabiu Kwankwaso kuma ina ganinsa a matsayin jiga-jigan dan siyasar da muke da su a kasar nan da ke samun ci gaba.

“Duk da haka, ban yarda da furucin da ya yi kwanan nan ba a lokacin da yake tattaunawa da shi a Kano, inda ya ce ya fi Peter Obi girma a siyasance. Idan aka dubi sakamakon zaben shugaban kasa na 2023, Peter Obi ya samu kuri’u 6,101,533 kuma ya yi nasara a jahohi 11, wanda ke nuna cewa ya samu goyon baya a kasatr nan. Sabanin yadda Sanata Kwankwaso ya samu kuri’u 1,496,687, wanda ya yi nasara a jiha daya kacal, Kano.

“Wadannan alkaluma sun nuna karara cewa, a kalla a yanayin zaben 2023, Peter Obi yana da matukar tasiri a siyasance a fadin kasar nan.

“Don haka Peter Obi ya fi Rabiu Kwankwaso girma a siyasance.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

Xi Jinping Ya Gana Da Mahalarta Taron Sada Zumunta Tsakanin Sin Da Ketare

LABARAI MASU NASABA

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.