• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye Kan Gudummawar Kasar Sin Game Da Ingiza Hadin Gwiwa Don Bunkasa Shawarar Raya Ci Gaban Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Waiwaye Kan Gudummawar Kasar Sin Game Da Ingiza Hadin Gwiwa Don Bunkasa Shawarar Raya Ci Gaban Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Samar da ci gaban rayuwa buri ne na daukacin bil adama. Kaza lika, daya ne daga muhimman ginshikai da daukacin kasashen duniya ke fatan cimmawa, kuma manufa ce da ba a kawo karshenta a tsawon tarihin rayuwar dan Adam a doron kasa.

 

Tun bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar nan ta raya ci gaban duniya wato “Global Development Initiative” ko GDI a takaice, yayin zaman muhawara na babban taron MDD karo na 76 a watan Satumban shekarar 2021, Sin ta ci gaba da samar da gudummawa bisa basirarta da karfinta na tunkarar batutuwan ci gaban kasa da kasa. A bana shekaru 3 ke nan bayan gabatar da wannan shawara ta GDI, kuma har yanzu ana ta kokarin karfafa matakan cimma nasararta.

  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Mai Nazarin Duniyar Dan Adam
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Kwamitin Kasa Na Shirya Liyafar Karrama Gwaraza A Fannin Raya Alakar Sin Da Amurka

Baya ga kasar Sin da ta gabatar da shawarar GDI, sassan kasa da kasa na ci gaba da rungumar shawarar, kawo yanzu kasashe da hukumomin kasa da kasa da suka nuna goyon bayansu ga wannan shawara sun haura 100, suna kuma ci gaba da karuwa, baya ga kasashe sama da 80 da suka shiga kawancen tabbatar da nasarar wannan shawara.

 

Labarai Masu Nasaba

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Masharhanta na jinjinawa kwazon kasar Sin bisa aiki da take yi tukuru tare da sauran abokan tafiya, musamman ganin yadda karkashin wannan shawara ta GDI, Sin ke ta fadada zuba jari ga ayyukan da suka shafi shawarar, inda adadin ayyukan bunkasa ci gaban duniya masu nasaba da ita suka zarce 1,000. Baya ga hakan, mun ga yadda Sin ta aiwatar da wasu ayyuka na hadin gwiwa tsakanin sassa 3, wato Sin da daidaikun kasashe, da kuma wasu hukumomin kasa da kasa da yawansu ya haura 140, ayyukan da aka gudanar da su a sama da kasashe 60.

 

Baya ga haka, kasar Sin ta samar da cibiyoyin horas da fasahohin kere-kere masu dacewa da aikin ingiza shawarar ta GDI, don baiwa dimbin al’ummun duniya damar cin gajiyar shawarar a kasashe masu tasowa. Bisa wannan shiri, an bude cibiyoyin koyar da sanin makaman aiki sama da 1,000 a irin wadannan kasashe, inda tuni kwararru sama da 40,000 suka ci gajiyar horo daga wadannan cibiyoyi.

 

Yayin da shawarar GDI ke samun tagomashi tsakanin sassan kasa da kasa, kuma take kara zurfafa hadin gwiwa da dukkanin sassa wajen yayata cin gajiya daga gare ta, ko shakka babu duniya za ta ci gaba da more damammakin zamanintarwa irin na kasar Sin, a daya hannu Sin da sauran sassan duniya za su ci gaba da dunkule wajen raba gajiyarsu.

 

Fatan dukkanin sassan kasa da kasa dai shi ne shawarar GDI, da makamantanta za su ci gaba da cimma nasara, su kuma dunkule tare da manyan manufofin bunkasa duniya, irinsu ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan zuwa shekarar 2030, da ajandar bunkasa kasashen Afirka ta kungiyar AU ta nan da shekarar 2063 da sauransu, ta yadda kasar Sin da sauran sassan kasa da kasa, za su kai ga kara ingiza ci gaban duniya bisa daidaito, da adalci, har a kai ga gina duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin

Next Post

A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

Related

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

16 hours ago
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

17 hours ago
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO
Daga Birnin Sin

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

18 hours ago
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire
Daga Birnin Sin

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

19 hours ago
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

20 hours ago
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

21 hours ago
Next Post
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.