ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye Kan Gudummawar Kasar Sin Game Da Ingiza Hadin Gwiwa Don Bunkasa Shawarar Raya Ci Gaban Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Samar da ci gaban rayuwa buri ne na daukacin bil adama. Kaza lika, daya ne daga muhimman ginshikai da daukacin kasashen duniya ke fatan cimmawa, kuma manufa ce da ba a kawo karshenta a tsawon tarihin rayuwar dan Adam a doron kasa.

 

Tun bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar nan ta raya ci gaban duniya wato “Global Development Initiative” ko GDI a takaice, yayin zaman muhawara na babban taron MDD karo na 76 a watan Satumban shekarar 2021, Sin ta ci gaba da samar da gudummawa bisa basirarta da karfinta na tunkarar batutuwan ci gaban kasa da kasa. A bana shekaru 3 ke nan bayan gabatar da wannan shawara ta GDI, kuma har yanzu ana ta kokarin karfafa matakan cimma nasararta.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Mai Nazarin Duniyar Dan Adam
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Kwamitin Kasa Na Shirya Liyafar Karrama Gwaraza A Fannin Raya Alakar Sin Da Amurka

Baya ga kasar Sin da ta gabatar da shawarar GDI, sassan kasa da kasa na ci gaba da rungumar shawarar, kawo yanzu kasashe da hukumomin kasa da kasa da suka nuna goyon bayansu ga wannan shawara sun haura 100, suna kuma ci gaba da karuwa, baya ga kasashe sama da 80 da suka shiga kawancen tabbatar da nasarar wannan shawara.

 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Masharhanta na jinjinawa kwazon kasar Sin bisa aiki da take yi tukuru tare da sauran abokan tafiya, musamman ganin yadda karkashin wannan shawara ta GDI, Sin ke ta fadada zuba jari ga ayyukan da suka shafi shawarar, inda adadin ayyukan bunkasa ci gaban duniya masu nasaba da ita suka zarce 1,000. Baya ga hakan, mun ga yadda Sin ta aiwatar da wasu ayyuka na hadin gwiwa tsakanin sassa 3, wato Sin da daidaikun kasashe, da kuma wasu hukumomin kasa da kasa da yawansu ya haura 140, ayyukan da aka gudanar da su a sama da kasashe 60.

 

Baya ga haka, kasar Sin ta samar da cibiyoyin horas da fasahohin kere-kere masu dacewa da aikin ingiza shawarar ta GDI, don baiwa dimbin al’ummun duniya damar cin gajiyar shawarar a kasashe masu tasowa. Bisa wannan shiri, an bude cibiyoyin koyar da sanin makaman aiki sama da 1,000 a irin wadannan kasashe, inda tuni kwararru sama da 40,000 suka ci gajiyar horo daga wadannan cibiyoyi.

 

Yayin da shawarar GDI ke samun tagomashi tsakanin sassan kasa da kasa, kuma take kara zurfafa hadin gwiwa da dukkanin sassa wajen yayata cin gajiya daga gare ta, ko shakka babu duniya za ta ci gaba da more damammakin zamanintarwa irin na kasar Sin, a daya hannu Sin da sauran sassan duniya za su ci gaba da dunkule wajen raba gajiyarsu.

 

Fatan dukkanin sassan kasa da kasa dai shi ne shawarar GDI, da makamantanta za su ci gaba da cimma nasara, su kuma dunkule tare da manyan manufofin bunkasa duniya, irinsu ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan zuwa shekarar 2030, da ajandar bunkasa kasashen Afirka ta kungiyar AU ta nan da shekarar 2063 da sauransu, ta yadda kasar Sin da sauran sassan kasa da kasa, za su kai ga kara ingiza ci gaban duniya bisa daidaito, da adalci, har a kai ga gina duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama.(Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.