ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Waiwaye Kan Gudummawar Kasar Sin Game Da Ingiza Hadin Gwiwa Don Bunkasa Shawarar Raya Ci Gaban Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Samar da ci gaban rayuwa buri ne na daukacin bil adama. Kaza lika, daya ne daga muhimman ginshikai da daukacin kasashen duniya ke fatan cimmawa, kuma manufa ce da ba a kawo karshenta a tsawon tarihin rayuwar dan Adam a doron kasa.

 

Tun bayan da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar nan ta raya ci gaban duniya wato “Global Development Initiative” ko GDI a takaice, yayin zaman muhawara na babban taron MDD karo na 76 a watan Satumban shekarar 2021, Sin ta ci gaba da samar da gudummawa bisa basirarta da karfinta na tunkarar batutuwan ci gaban kasa da kasa. A bana shekaru 3 ke nan bayan gabatar da wannan shawara ta GDI, kuma har yanzu ana ta kokarin karfafa matakan cimma nasararta.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Mai Nazarin Duniyar Dan Adam
  • Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Kwamitin Kasa Na Shirya Liyafar Karrama Gwaraza A Fannin Raya Alakar Sin Da Amurka

Baya ga kasar Sin da ta gabatar da shawarar GDI, sassan kasa da kasa na ci gaba da rungumar shawarar, kawo yanzu kasashe da hukumomin kasa da kasa da suka nuna goyon bayansu ga wannan shawara sun haura 100, suna kuma ci gaba da karuwa, baya ga kasashe sama da 80 da suka shiga kawancen tabbatar da nasarar wannan shawara.

 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Masharhanta na jinjinawa kwazon kasar Sin bisa aiki da take yi tukuru tare da sauran abokan tafiya, musamman ganin yadda karkashin wannan shawara ta GDI, Sin ke ta fadada zuba jari ga ayyukan da suka shafi shawarar, inda adadin ayyukan bunkasa ci gaban duniya masu nasaba da ita suka zarce 1,000. Baya ga hakan, mun ga yadda Sin ta aiwatar da wasu ayyuka na hadin gwiwa tsakanin sassa 3, wato Sin da daidaikun kasashe, da kuma wasu hukumomin kasa da kasa da yawansu ya haura 140, ayyukan da aka gudanar da su a sama da kasashe 60.

 

Baya ga haka, kasar Sin ta samar da cibiyoyin horas da fasahohin kere-kere masu dacewa da aikin ingiza shawarar ta GDI, don baiwa dimbin al’ummun duniya damar cin gajiyar shawarar a kasashe masu tasowa. Bisa wannan shiri, an bude cibiyoyin koyar da sanin makaman aiki sama da 1,000 a irin wadannan kasashe, inda tuni kwararru sama da 40,000 suka ci gajiyar horo daga wadannan cibiyoyi.

 

Yayin da shawarar GDI ke samun tagomashi tsakanin sassan kasa da kasa, kuma take kara zurfafa hadin gwiwa da dukkanin sassa wajen yayata cin gajiya daga gare ta, ko shakka babu duniya za ta ci gaba da more damammakin zamanintarwa irin na kasar Sin, a daya hannu Sin da sauran sassan duniya za su ci gaba da dunkule wajen raba gajiyarsu.

 

Fatan dukkanin sassan kasa da kasa dai shi ne shawarar GDI, da makamantanta za su ci gaba da cimma nasara, su kuma dunkule tare da manyan manufofin bunkasa duniya, irinsu ajandar wanzar da ci gaba ta MDD ta nan zuwa shekarar 2030, da ajandar bunkasa kasashen Afirka ta kungiyar AU ta nan da shekarar 2063 da sauransu, ta yadda kasar Sin da sauran sassan kasa da kasa, za su kai ga kara ingiza ci gaban duniya bisa daidaito, da adalci, har a kai ga gina duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama.(Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

A Farfado Da Rayuwar Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.