ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
Yansanda

Kwamishinan ‘Yansanda na Babban Birnin Tarayya (FCT), CP Ajao Adewale, ya gargadi jami’an ‘yansanda da na kula da zirga-zirga kan yin tsalle cikin motocin da ke tafe ko kuma jan sitiyarin direbobi, yana mai bayyana irin wannan hali a matsayin abin da bai da tsaro, bai dace ba, kuma yana lalata mutuncin Rundunar ‘Yansanda ta Najeriya (NPF).

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ‘yansandan FCT, SP Josephine Adeh, ta fitar a Abuja, ta ce Kwamishinan ‘Yansanda ya yi Allah-wadai da dabi’ar rashin kwarewa ta jami’an zirga-zirga na yin tsalle cikin motocin masu karya doka ko kuma yunkurin kwace sitiyarin direbobi. CP ya bayyana irin wadannan ayyuka a matsayin masu hadari, da ba za a aminta da su ba, kuma ya sabawa ka’idojin aikin ‘yansanda.

Adeh ta ce CP ya kuma sanar da kaddamar da aikin musamman mai suna Operation Keep Traffic Flowing, inda aka kafa tawagar sa ido domin tabbatar da bin wannan umarni, tare da gargadin cewa duk jami’in da aka samu yana keta wadannan dokoki za a hukunta shi.

ADVERTISEMENT

“CP ya bayyana fara aikin gaggawa na Operation ‘Keep Traffic Flowing’, kuma ya kafa tawagar sintiri domin bibiyar ayyukan jami’an zirga-zirga gaba kaya, tare da umarni na musamman kan kama duk wani jami’i da aka samu da karya wannan doka,” in ji ta.

Hakazalika, CP ya bayyana muhimman wuraren da ke da cunkoson zirga-zirga a Abuja, ya kuma gargadi jami’an sintiri kan gujewa dabi’ar rashin kwarewar yin tsalle cikin motocin masu laifi.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

A jawabin da ya yi wa shugabannin sashen sintiri, jami’an ‘yansandan motoci, da sauran jami’an da ke aiki a hedikwatar rundunar, CP ya ce halayen jami’an sintiri a fili suke bayyana hoton da al’umma ke da shi game da rundunar ‘yansanda.

Adeh ta bayyana cewa CP ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda jami’ai ke gudanar da ayyuka a halin yanzu, yana mai jaddada cewa kula da zirga-zirga na daga cikin manyan alamomin nuna ci gaban gari.

Bayan ya yi yawon duba wurare da dama a birnin a lokutan cunkoso, CP ya gano muhimman wurare kusan 30 da ke da matsalar zirga-zirga, ciki har da Wuse, Area 1 Roundabout, Jikwoyi, Karu, Kurudu, AYA, Apo Resettlement, Gudu, Galadima, Dawaki, da Kubwa.

Ya umarci jami’ai da su kasance a bayyane a wadannan wurare domin tabbatar da tafiyar zirga-zirga yadda ya kamata.

“CP Adewale ya bayyana rashin jin dadinsa kan yadda jami’an sintiri ke gudanar da aikinsu yanzu, yana mai jaddada bukatar sabuwar fahimtar aiki. Ya ce harkar sintiri na daga cikin muhimman alamu na auna tsari da ci gaban gari, yayin da jami’an zirga-zirga suke kasancewa hoton farko da jama’a ke gani daga ‘yansanda.

“A kan haka, ya gargade su da su kiyaye ladubban aiki da bin doka, su guji duk wani hali marar kyau da zai iya bata sunan rundunar gaba daya da kuma na FCT musamman,” in ji PPRO.

Ya kuma roki mazauna birnin da su bi dokokin zirga-zirga, su mutunta jami’an da ke bakin aiki, su kuma guji bayar da cin hanci, wanda ya bayyana a matsayin abin da bai dace ba. Ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da kasancewa a fili tare da tabbatar da ingantacciyar tafiyar zirga-zirga a FCT.

Yansanda
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji
Yansanda
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
  • Sulaiman
    Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki
  • Sulaiman
    Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna
Labarai

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Next Post
Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.