• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi Ko Dai Shiririta?

by Leadership Hausa
11 months ago
in Manyan Labarai
0
Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A zabubbukan kanannan hukumomi na kwanakin baya, da aka gudanar a wasu jihohin kasar nan, gwamnonin jihohin, sun yi ta hakilon yin karfakarafa domin ganin cewa, ko ta halin kaka, sai ‘yan takararar su ne, suka lashe zabubbukan.

Misali a makonni ukun da suka gatabata, an gudanar da zabubbukan kanannan hukumomi a jhohin Anambra, Kwara, Kebbi, Ribas, Biniwe, Akwa Ibom, Filato da dai, sauransu.

  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

Hakazalika, ma jihohin Kano da Kaduna, suna ci gaba da kai gwauro su kai mari, domin ganin sun dora ko nada ‘yan takarar jam’iyyunsu a zabubbukan shugagannin na kanannan hukumomin.

Hukumomin gudanar da zabubbukan na kananan hukumomi masu zaman kansu na jihohin da kundin tsarin mulki kasar na shekarar 1999 da aka sabunta, ya dora masu alhakin gudanar da dabubbukan bisa adalci.

Sai dai, kuma abin takaici, akasarin zabubbukan na kanannan hukumomin da aka gudanarwa, cike suke da tabka magudin da kusan ma ya wuce hankali.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Hakanan ma, wani da ya zama tamkar gari a yayin gudanar da zabubbukan na kanannan hukumomi a kasar shi ne, yadda jam’iyyar da ke rike da madabun iko a jihohin, galibi ‘yan takararta ne, suke lashe zabubbukan, kusan tun daga na shugaban karamar hukuma har zuwa na Kansiloli.

Sai dai kuma, an samu wani dan karamin sauyi a jihar Akwa Ibom, inda jam’iyyar adawa ta APC, ta lashe zaben karamar hukuma daya kacal a jihar.

An dai sha zargin gwamnonin jihohin wajen yin amfani da ‘yan korensu don yin karfa-karfar tabka magudin zabe.

Misali, a jihar Ribas, a zabubbukan kanannan hukumomi na jihar da aka yi bada dadewa ba, an zargi gwamnan jihar Siminalayi Fubara da tabka irin wannan kazamin magudin, zaben, inda jam’iyyar APP da goyawa baya a lokacin zaben, ta samu gaggarumar galaba, a kan sauran jam’iyyun adawa da suka fafata a zaben.

Jam’iyyar ta APP ta lashe zabubbukan ne, saboda goyon bayan da ta samu daga gun gwamna Fubara, ta hanyar nada masu yi masa biyayya a matsayin jami’an hukumar zaben jihar da suka gudanar da zabukan.

Bugu da kari kuma wadannan jami’an hukumar zaben, sun samu sahalewar ‘yan majalisar dokokin jihar da Fubura ke juya su kamar Waina, don su gudanar da zabubbukan tun daga Kujerar shugabannin kananan hukumimin har zuwa Kujerar Kansilpli.

A irin wadannan zabubbukan, cike suke da magudi da abin al’ajabi, domin tun kafin ma a sanar da sakamkon zabukan, aka fara taya ‘yan takarar jam’iyya mai mulki, murnar lashe zabe.

Yana da kyau a gane lamarin, duk da cewa, irin yakin da kanannan hukumomin kasar suka sha fama suna yi, na sai sun samu ‘yancin cin gashin kansu, wanda daga bisani, suka yi nasara bayan da kotun kolin kasar ta yanke hukuncin ba su damar cin gashin ‘yancin kansu, amma ga dukkan alamu, har yanzu kusan yakin bai kare baa kwai sauar rina a kaba.

Idan har yanzu ba a samar da tsarin gudanar da sahihan zabubbukan a kanannan hukumomi ba, idan aka lura da yadda gwamnonin jihohin ke yin amfani da dukkan karfin ikon da suke da shi don ganin ‘yan takarar jam’iyyun su, sun samu nasara, to za a iya cewa, tamkar an kashe Maciji ne, amma ba a sare kansa ba.

Amma domin a kawo karshen irin wannan kwamacalar a zabubbukan kanannan hukumomi, wannan jaridar, na son kara jaddada kiranta na a soke hukumomin gudanar da zabe masu zaman kansu na jihohi.

Maimakon haka ma sai a bar hukumomin zaben su rinka gudanar da zabubbuka, kamata ya yi a bai wa hukumar zabe maizaman kanta ikon gudanar da zabukan.

Irin wannan tabka magudin da dagewar da gwamnonin jihohin suke yi, na sai ‘yan takarar jam’iyyunsu sun lashe zabubbukan, ba zai sakarwa da shugabanninta mara ba don yiwa al’umomin su aiki, kamar yadda ya kamata ba.

Abin takaici ne, sai da goyon bayan gwamna ne, kawai dankarar kujerrar shugaban karamar hukuma ko kuma ta Kansila zai iya lashe zabe tare da amincewar wasu daga cikin jiga-jigan shugabannin jim’iyya mai ci.

Bugu da kari kuma, akasarin Kansilolin da suka lashe zabe, idan shugaban karamar hukumar ya aikata laifin da ya cancanci a tsaige shi, ba su da wani ikon iya tsige shi.

Duk wani darasin da aka koya na bai wa hukumomin zabe masu zaman kansu na jihohin kasar nan ragamar gudanar da zabubbukan, hakan na ci gaba da nuna cewa, har yanzu wadanda aka zaba a matsayin shugagabannin kanannan hukumomin, na ci gaba da kasancewa ‘yan amshin Shata ne, wato za su ci gaba da kasancewa ne a karkashin ikon gwamnonin saboda tsayuwar da suka yi tsayin daka, wajen ganin shugabannin, sun lashe zabubbukan, wanda kuma a dole ne, sai sun bi umarnin gwamnonin

Lamarin dai, babban abin kunya ne a harkar dimokiradaiyyar kasar nan musamman ma ganin yadda gwamnonin, ke yin amfani da hukumomin gudanar da zabubbukan jihohinsu, don su tabka magudin zabe, wanda kuma haka ne ke nunawa a zahiri cewar, zabubbukan tamkarwata shiririta ce kawai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ShiriritaZaben Kananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron BRICS Na Wannan Karo Ya Shaida Himmar Kasashe Mambobin Kungiyar Wajen Ingiza Zaman Lafiya A Duniya

Next Post

Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

1 hour ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

3 hours ago
An ÆŠauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya
Manyan Labarai

An ÆŠauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

5 hours ago
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

9 hours ago
majalisar kasa
Manyan Labarai

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

12 hours ago
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama
Manyan Labarai

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

1 day ago
Next Post
Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna...

LABARAI MASU NASABA

“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

“Hadin Kan Kasashen BRICS” Ya Karfafa Shawo Kan Kalubale

September 10, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

September 10, 2025
Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

September 10, 2025
Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

September 10, 2025
Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

September 10, 2025
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

September 10, 2025
Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

September 10, 2025
An ÆŠauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

An ÆŠauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

September 10, 2025
Mun KaÉ—u MatuÆ™a Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.