• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi Ko Dai Shiririta?

by Leadership Hausa
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A zabubbukan kanannan hukumomi na kwanakin baya, da aka gudanar a wasu jihohin kasar nan, gwamnonin jihohin, sun yi ta hakilon yin karfakarafa domin ganin cewa, ko ta halin kaka, sai ‘yan takararar su ne, suka lashe zabubbukan.

Misali a makonni ukun da suka gatabata, an gudanar da zabubbukan kanannan hukumomi a jhohin Anambra, Kwara, Kebbi, Ribas, Biniwe, Akwa Ibom, Filato da dai, sauransu.

  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

Hakazalika, ma jihohin Kano da Kaduna, suna ci gaba da kai gwauro su kai mari, domin ganin sun dora ko nada ‘yan takarar jam’iyyunsu a zabubbukan shugagannin na kanannan hukumomin.

Hukumomin gudanar da zabubbukan na kananan hukumomi masu zaman kansu na jihohin da kundin tsarin mulki kasar na shekarar 1999 da aka sabunta, ya dora masu alhakin gudanar da dabubbukan bisa adalci.

Sai dai, kuma abin takaici, akasarin zabubbukan na kanannan hukumomin da aka gudanarwa, cike suke da tabka magudin da kusan ma ya wuce hankali.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hakanan ma, wani da ya zama tamkar gari a yayin gudanar da zabubbukan na kanannan hukumomi a kasar shi ne, yadda jam’iyyar da ke rike da madabun iko a jihohin, galibi ‘yan takararta ne, suke lashe zabubbukan, kusan tun daga na shugaban karamar hukuma har zuwa na Kansiloli.

Sai dai kuma, an samu wani dan karamin sauyi a jihar Akwa Ibom, inda jam’iyyar adawa ta APC, ta lashe zaben karamar hukuma daya kacal a jihar.

An dai sha zargin gwamnonin jihohin wajen yin amfani da ‘yan korensu don yin karfa-karfar tabka magudin zabe.

Misali, a jihar Ribas, a zabubbukan kanannan hukumomi na jihar da aka yi bada dadewa ba, an zargi gwamnan jihar Siminalayi Fubara da tabka irin wannan kazamin magudin, zaben, inda jam’iyyar APP da goyawa baya a lokacin zaben, ta samu gaggarumar galaba, a kan sauran jam’iyyun adawa da suka fafata a zaben.

Jam’iyyar ta APP ta lashe zabubbukan ne, saboda goyon bayan da ta samu daga gun gwamna Fubara, ta hanyar nada masu yi masa biyayya a matsayin jami’an hukumar zaben jihar da suka gudanar da zabukan.

Bugu da kari kuma wadannan jami’an hukumar zaben, sun samu sahalewar ‘yan majalisar dokokin jihar da Fubura ke juya su kamar Waina, don su gudanar da zabubbukan tun daga Kujerar shugabannin kananan hukumimin har zuwa Kujerar Kansilpli.

A irin wadannan zabubbukan, cike suke da magudi da abin al’ajabi, domin tun kafin ma a sanar da sakamkon zabukan, aka fara taya ‘yan takarar jam’iyya mai mulki, murnar lashe zabe.

Yana da kyau a gane lamarin, duk da cewa, irin yakin da kanannan hukumomin kasar suka sha fama suna yi, na sai sun samu ‘yancin cin gashin kansu, wanda daga bisani, suka yi nasara bayan da kotun kolin kasar ta yanke hukuncin ba su damar cin gashin ‘yancin kansu, amma ga dukkan alamu, har yanzu kusan yakin bai kare baa kwai sauar rina a kaba.

Idan har yanzu ba a samar da tsarin gudanar da sahihan zabubbukan a kanannan hukumomi ba, idan aka lura da yadda gwamnonin jihohin ke yin amfani da dukkan karfin ikon da suke da shi don ganin ‘yan takarar jam’iyyun su, sun samu nasara, to za a iya cewa, tamkar an kashe Maciji ne, amma ba a sare kansa ba.

Amma domin a kawo karshen irin wannan kwamacalar a zabubbukan kanannan hukumomi, wannan jaridar, na son kara jaddada kiranta na a soke hukumomin gudanar da zabe masu zaman kansu na jihohi.

Maimakon haka ma sai a bar hukumomin zaben su rinka gudanar da zabubbuka, kamata ya yi a bai wa hukumar zabe maizaman kanta ikon gudanar da zabukan.

Irin wannan tabka magudin da dagewar da gwamnonin jihohin suke yi, na sai ‘yan takarar jam’iyyunsu sun lashe zabubbukan, ba zai sakarwa da shugabanninta mara ba don yiwa al’umomin su aiki, kamar yadda ya kamata ba.

Abin takaici ne, sai da goyon bayan gwamna ne, kawai dankarar kujerrar shugaban karamar hukuma ko kuma ta Kansila zai iya lashe zabe tare da amincewar wasu daga cikin jiga-jigan shugabannin jim’iyya mai ci.

Bugu da kari kuma, akasarin Kansilolin da suka lashe zabe, idan shugaban karamar hukumar ya aikata laifin da ya cancanci a tsaige shi, ba su da wani ikon iya tsige shi.

Duk wani darasin da aka koya na bai wa hukumomin zabe masu zaman kansu na jihohin kasar nan ragamar gudanar da zabubbukan, hakan na ci gaba da nuna cewa, har yanzu wadanda aka zaba a matsayin shugagabannin kanannan hukumomin, na ci gaba da kasancewa ‘yan amshin Shata ne, wato za su ci gaba da kasancewa ne a karkashin ikon gwamnonin saboda tsayuwar da suka yi tsayin daka, wajen ganin shugabannin, sun lashe zabubbukan, wanda kuma a dole ne, sai sun bi umarnin gwamnonin

Lamarin dai, babban abin kunya ne a harkar dimokiradaiyyar kasar nan musamman ma ganin yadda gwamnonin, ke yin amfani da hukumomin gudanar da zabubbukan jihohinsu, don su tabka magudin zabe, wanda kuma haka ne ke nunawa a zahiri cewar, zabubbukan tamkarwata shiririta ce kawai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ShiriritaZaben Kananan Hukumomi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron BRICS Na Wannan Karo Ya Shaida Himmar Kasashe Mambobin Kungiyar Wajen Ingiza Zaman Lafiya A Duniya

Next Post

Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

8 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

9 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

17 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

22 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

1 day ago
Next Post
Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna...

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.