ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Kananan Hukumomi Ko Dai Shiririta?

by Leadership Hausa
2 years ago
A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

A woman votes at a polling station in Kano, Nigeria, March 28, 2015. Many Nigerians fear a clash along religious, ethnic, and sectional lines regardless of the result of the presidential race between incumbent Goodluck Jonathan, a Christian from the south, and Muhammadu Buhari, a former military ruler and Muslim northerner. (Samuel Aranda/The New York Times)

A zabubbukan kanannan hukumomi na kwanakin baya, da aka gudanar a wasu jihohin kasar nan, gwamnonin jihohin, sun yi ta hakilon yin karfakarafa domin ganin cewa, ko ta halin kaka, sai ‘yan takararar su ne, suka lashe zabubbukan.

Misali a makonni ukun da suka gatabata, an gudanar da zabubbukan kanannan hukumomi a jhohin Anambra, Kwara, Kebbi, Ribas, Biniwe, Akwa Ibom, Filato da dai, sauransu.

  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?
  • Me Najeriya Za Ta Iya Samu Daga Tsarin BRICS?

Hakazalika, ma jihohin Kano da Kaduna, suna ci gaba da kai gwauro su kai mari, domin ganin sun dora ko nada ‘yan takarar jam’iyyunsu a zabubbukan shugagannin na kanannan hukumomin.

ADVERTISEMENT

Hukumomin gudanar da zabubbukan na kananan hukumomi masu zaman kansu na jihohin da kundin tsarin mulki kasar na shekarar 1999 da aka sabunta, ya dora masu alhakin gudanar da dabubbukan bisa adalci.

Sai dai, kuma abin takaici, akasarin zabubbukan na kanannan hukumomin da aka gudanarwa, cike suke da tabka magudin da kusan ma ya wuce hankali.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Hakanan ma, wani da ya zama tamkar gari a yayin gudanar da zabubbukan na kanannan hukumomi a kasar shi ne, yadda jam’iyyar da ke rike da madabun iko a jihohin, galibi ‘yan takararta ne, suke lashe zabubbukan, kusan tun daga na shugaban karamar hukuma har zuwa na Kansiloli.

Sai dai kuma, an samu wani dan karamin sauyi a jihar Akwa Ibom, inda jam’iyyar adawa ta APC, ta lashe zaben karamar hukuma daya kacal a jihar.

An dai sha zargin gwamnonin jihohin wajen yin amfani da ‘yan korensu don yin karfa-karfar tabka magudin zabe.

Misali, a jihar Ribas, a zabubbukan kanannan hukumomi na jihar da aka yi bada dadewa ba, an zargi gwamnan jihar Siminalayi Fubara da tabka irin wannan kazamin magudin, zaben, inda jam’iyyar APP da goyawa baya a lokacin zaben, ta samu gaggarumar galaba, a kan sauran jam’iyyun adawa da suka fafata a zaben.

Jam’iyyar ta APP ta lashe zabubbukan ne, saboda goyon bayan da ta samu daga gun gwamna Fubara, ta hanyar nada masu yi masa biyayya a matsayin jami’an hukumar zaben jihar da suka gudanar da zabukan.

Bugu da kari kuma wadannan jami’an hukumar zaben, sun samu sahalewar ‘yan majalisar dokokin jihar da Fubura ke juya su kamar Waina, don su gudanar da zabubbukan tun daga Kujerar shugabannin kananan hukumimin har zuwa Kujerar Kansilpli.

A irin wadannan zabubbukan, cike suke da magudi da abin al’ajabi, domin tun kafin ma a sanar da sakamkon zabukan, aka fara taya ‘yan takarar jam’iyya mai mulki, murnar lashe zabe.

Yana da kyau a gane lamarin, duk da cewa, irin yakin da kanannan hukumomin kasar suka sha fama suna yi, na sai sun samu ‘yancin cin gashin kansu, wanda daga bisani, suka yi nasara bayan da kotun kolin kasar ta yanke hukuncin ba su damar cin gashin ‘yancin kansu, amma ga dukkan alamu, har yanzu kusan yakin bai kare baa kwai sauar rina a kaba.

Idan har yanzu ba a samar da tsarin gudanar da sahihan zabubbukan a kanannan hukumomi ba, idan aka lura da yadda gwamnonin jihohin ke yin amfani da dukkan karfin ikon da suke da shi don ganin ‘yan takarar jam’iyyun su, sun samu nasara, to za a iya cewa, tamkar an kashe Maciji ne, amma ba a sare kansa ba.

Amma domin a kawo karshen irin wannan kwamacalar a zabubbukan kanannan hukumomi, wannan jaridar, na son kara jaddada kiranta na a soke hukumomin gudanar da zabe masu zaman kansu na jihohi.

Maimakon haka ma sai a bar hukumomin zaben su rinka gudanar da zabubbuka, kamata ya yi a bai wa hukumar zabe maizaman kanta ikon gudanar da zabukan.

Irin wannan tabka magudin da dagewar da gwamnonin jihohin suke yi, na sai ‘yan takarar jam’iyyunsu sun lashe zabubbukan, ba zai sakarwa da shugabanninta mara ba don yiwa al’umomin su aiki, kamar yadda ya kamata ba.

Abin takaici ne, sai da goyon bayan gwamna ne, kawai dankarar kujerrar shugaban karamar hukuma ko kuma ta Kansila zai iya lashe zabe tare da amincewar wasu daga cikin jiga-jigan shugabannin jim’iyya mai ci.

Bugu da kari kuma, akasarin Kansilolin da suka lashe zabe, idan shugaban karamar hukumar ya aikata laifin da ya cancanci a tsaige shi, ba su da wani ikon iya tsige shi.

Duk wani darasin da aka koya na bai wa hukumomin zabe masu zaman kansu na jihohin kasar nan ragamar gudanar da zabubbukan, hakan na ci gaba da nuna cewa, har yanzu wadanda aka zaba a matsayin shugagabannin kanannan hukumomin, na ci gaba da kasancewa ‘yan amshin Shata ne, wato za su ci gaba da kasancewa ne a karkashin ikon gwamnonin saboda tsayuwar da suka yi tsayin daka, wajen ganin shugabannin, sun lashe zabubbukan, wanda kuma a dole ne, sai sun bi umarnin gwamnonin

Lamarin dai, babban abin kunya ne a harkar dimokiradaiyyar kasar nan musamman ma ganin yadda gwamnonin, ke yin amfani da hukumomin gudanar da zabubbukan jihohinsu, don su tabka magudin zabe, wanda kuma haka ne ke nunawa a zahiri cewar, zabubbukan tamkarwata shiririta ce kawai.

Zaben
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna...

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.