ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar MAAUN Da Kwalejin Seneca ta Canada Sun Yi Haɗin Gwiwa Domin Samar Da Damarmaki Ga Ɗalibai A Duniya

by Bello Hamza and Sulaiman
10 months ago
MAAUN

Gamayyar rukunin jami’o’in MAAUN ta kulla yarjejeniyar hadin gwiwar kasa da kasa da ‘Seneca College of Applied Arts and Technology’ da ke kasar Canada, wacce aka tabbatar da wannan alaka ta hanyar rattaba hannu kan wata yarjejeniya domin inganta koyar da harshen Turanci, musayar dalibai, da hadin gwiwa na tsare-tsaren ilimi.

 

Rukunin MAAUN, wanda ya kunshi Jami’ar ‘Canadian University of Nigeria’ da ke Abuja, Franco British International University da ke Kaduna, Maryam Abacha American University da ke Maradi a Jamhuriyar Nijar, da Maryam Abacha American University da ke Kano, na neman fadada tasirinta a duniya ta hanyar wannan hadin gwiwar.

ADVERTISEMENT
  • Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing
  • INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

An sanya hannu kan yarjejeniyar ne a ranar Alhamis, 4 ga Satumba, 2025, inda Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo, wanda ya kafa kuma Shugaban rukunin jami’o’in MAAUN, ya wakilci jami’o’in guda hudu, a yayin da David Agnew ya sanya hannu a madadin Seneca College.

 

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

A yayin taron rattaba hannun, Farfesa Gwarzo ya bayyana manufar wannan yarjejeniya, inda ya ce hadin gwiwar za ta bai wa dalibai da ma’aikata damar cin moriyar albarkatu da kwarewa daga kasashen waje.

 

“Wannan hadin gwiwar alama ce ta jajircewarmu wajen hada jami’o’inmu da manyan cibiyoyi na duniya domin bunkasa kirkire-kirkire da bincike a rukunin jami’o’inmu na MAAUN,” in ji shi.

 

A karkashin wannan yarjejeniyar, cibiyoyin biyu za su rika raba kwarewar su tare da tallafa wa juna don cimma manufofi na bai daya. Muhimman bangarorin hadin gwiwar sun hada da samar da koyarwar harshen Turanci ta yanar gizo ga daliban MAAUN, samar da hanyoyi don ci gaba da karatu a Seneca, da bayar da shawarwari kan harkokin ilimi ga ma’aikatan MAAUN.

 

Haka kuma, yarjejeniyar ta tanadi shirye-shiryen kirkiro da karatun hadin gwiwa, inda za a tantance irin takardar shaidar da za a bayar, tsawon lokacin karatu, da kuma bangaren da shirin za a mayar da hankali wanda cibiyoyin biyu za su sahhale.

Bugu da kari, yarjejeniyar ta tanadi dabarun inganta damar samun ilimi a Seneca ga daliban da ke cikin rukunin jami’o’in MAAUN tare da wasu bangarori na hadin gwiwar da za a iya yi a nan gaba.

 

Farfesa Gwarzo ya nuna kwarin gwiwarsa game da dogon tasirin wannan hadin gwiwa, inda ya jaddada cewa yarjejeniyar za ta zama ginshiki wajen tabbatar da ci gaba mai dorewa.

 

“Muna da niyyar aiwatar da wannan yarjejeniya cikin cikakken tsari domin bunkasa bincike da kirkire-kirkire tare da cimma manufofin da aka tsara. Wannan muhimmin mataki ne wajen karfafa ingancin ilimi a jami’o’inmu,” in ji shi.

Wannan yarjejeniyar na nuni da kokarin da gamayyar rukunin jami’o’in MAAUN ke yi na fadada hadin gwiwa da sauran cibiyoyi a duniya, domin tabbatar da cewa dalibai da ma’aikata sun amfana daga kwarewa da horo na kasa da kasa, tare da karfafa damar gudanar da bincike da kirkire-kirkire a rukunin jami’o’i.

MAAUN
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
MAAUN
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu
  • Sulaiman
    Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa
  • Sulaiman
    An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara
  • Sulaiman
    2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
Labarai

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Next Post
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026
Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu

Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu

July 12, 2026
Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.