• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?

by Abba Ibrahim Wada
7 months ago
in Wasanni
0
Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kyaftin din tawagar Super Eagles ta Nijeriya kuma dan wasan da yafi buga wa kasar wasanni a tarihi Ahmed Musa na ci gaba da taka rawar gani a wasannin da yake bugawa tun bayan komawarsa tsohuwar kungiyarshi ta Kano Pillars a watan jiya, Musa ya dade bai buga wa Nijeriya wasa ba duk da cewa shi ne kyaftin din tawagar a halin yanzu sakamakon rashin kungiya na tsawon lokaci.

A gasar cin kofin nahiyoyi da hukumar kwallon kafa ta FIFA ta shirya a shekarar 2013 Musa ya fara buga wa Nijeriya kwallo, inda ya buga dukkan wasannin guda uku da Nijeriya ta buga a gasar yayin da aka fitar da su tun a matakin rukuni.

  • Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (3)
  • Tinubu Ya Naɗa Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Bayan buga dukkan wasannin share fage, an saka sunan Musa a cikin tawagar Nijeriya wadda Stephen Keshi ke jagoranta a wancan lokaci domin buga gasar cin kofin duniya na shekarar 2014, Musa ya zura kwallaye biyu a wasan karshe na rukunin F inda Nijeriya ta yi rashin nasara da ci 3–2 a hannun kasar Argentina.

A watan Oktobar shekarar 2015, bayan ritayar Bincent Enyeama daga buga kwallon kafa, kocin Nijeriya, Sunday Oliseh ya nada Musa a matsayin kyaftin din tawagar sai dai an sauya wannan shawarar a shekarar 2016 yayin da aka nada Mikel John Obi a matsayin kyaftin din tawagar Nijeriya Musa kuma ya koma matsayin mataimakin Kyaftin.

A watan Mayun 2018 an saka shi cikin jerin ‘yan wasa 30 na farko da za su wakilci Nijeriya a gasar cin kofin duniya ta FIFA 2018 a kasar Rasha, Musa ya matukar taka rawar gani a wasansu da kasar Iceland inda ya jefa kwallo biyu a ragar turawan, amma hakan bai hana Nijeriya ficewa daga gasar ba sakamakon rashin nasara da suka yi a hannun Argentina.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

A watan Yunin shekarar 2019 Musa ya zama dan wasa na uku da ya fi taka leda a tarihin tawagar Super Eagles inda ya zarce Nwankwo Kanu, Musa ya zama dan Nijeriya na farko da ya ci fiye da kwallo daya a gasar cin kofin duniya ta FIFA, bayan ya zura kwallaye biyu a ragar Argentina a gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2014.

Musa kuma shi ne dan Nijeriya na farko da ya zura kwallo a gasar cin kofin duniya ta FIFA guda biyu, bayan ya zura kwallaye biyu a ragar Iceland a matakin rukuni na gasar cin kofin duniya ta FIFA 2018, jimilla ya buga wasanni 108, shi ne dan wasan da ya fi buga wa Nijeriya wasa a tarihi.

Wasan karshe da Musa ya buga wa Nijeriya shi ne wanda ya shigo a minti na 94 a fafatawar neman buga gasar kasashen nahiyar Afirika a tsakaninsu da Guinea Bissau ranar 27 ga watan Maris na shekarar 2023,amma ya na cikin ‘yan wasan da suka wakilci Nijeriya a gasar kasashen nahiyar Afirika da aka buga a kasar Kwaddibowa inda aka doke Nijeriya a wasan karshe da ci 1-0,duk da cewar Musa bai buga wasa ko daya ba har aka kammala gasar ya matukar taimaka wa ‘yan wasan Nijeriya da shawarwarin irin nasu na tsoffin kanu a harkar kwallon kafa.

Tun bayan dawowarshi Kano Pillars da take leda Musa ya zura kwallaye uku ya taimaka aka zura biyu a wasanni 4 da ya bugawa Sai Masu Gida, hakan ya sa ake tunanin ya dawo da rigarshi ta tawagar Nijeriya da ya rasa na tsawon lokaci idan ya ci gaba da taka rawar gani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ahmed MusaRIgaSuper EaglesWasanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Ji Dadin Abin Da Ya Faru Da Tawagar ‘Super Eagles’ A Libya Ba -Patrice Motsepe

Next Post

Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

3 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

3 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

5 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

6 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

6 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

Gwamna Sani Ya Samu Karramawa Daga Igbo, Ya Bayar Da Fili Don Gina Kasuwar Kayayyakin Gyara

LABARAI MASU NASABA

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 14, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.