• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ba Za Ta Samu Wani Sabon Bashi Daga Bankin AfDB Ba -Farfesa Oyebanji

by Abubakar Abba and Sulaiman
12 months ago
AFDB

Nijeriya za ta yi asarar samun wani sabon bashin a zango na biyu, kan kafa masana’antun noma na shiyya-shiyya (SAPZs).

Kasar za ta yi wannan asara ce, sakamakon jinkirin da aka samu na rashin wanzar da zango na daya na shirin, wanda yawan bashin ya kai kimanin dala miliyan 38.
Babban mai bai wa Shugaban Bankin Raya Nahiyar Afrika (AFDB), Dakta Akinwumi Adesina, Farfesa Oyebanji Oyelaran-Oyeyinka ne ya bayyana hakan.

  • Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano
  • Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Farfesan, ya sanar da hakan ne a lokacin da ya gabatar da wata kasida ta shiri na musamman kan kafa masana’antun noma na shiyya-shiyya a wani taron bita na jihohin da suka amfana da kashin farko na shirin da aka gudanar a A.

Ya ce, ma’anar shirin; wata dabara ce ta zamani da za ta taimaka wa Nijeriya wajen fitar da ita daga matsalar rashin aikin yi da kasar ke fuskanta a halin yanzu.

Oyebanji ya kuma yi nuni da cewa, duba da jinkirin da ake fuskanta na wanzar da shirin kashi na daya tare da shirye-shiryen barin ofis na Dakta Akinwumi Adesina, a matsayin shugaban bankin; nan da shekaru biyu, hakan zai sa Nijeriya ta sake neman sake ciwo wani bashin daga bankin.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Har ila yau, ya kuma yi gargadin cewa; matukar Nijeriya ba ta tashi tsaye ba, zai yi wuya ta samu bashin a zango na biyu.
Haka zalika, sai dai wata majiya ta tabbatar da cewa; ba a wanzar da wannan shiri ba, sakamakon guda daga cikin ministocin a wancan lokaci ya soki shirin a wani zama da majalisar zartarwa ta wancan lokacin ta yi.

Amma duk da haka, bayan Dakta Adesina ya zama shugaban bankin AFDB, ya wanzar da shirin; inda bankin ya rika taimaka wa kasashe da dama ciki har da Kasar Ethiopia, wanda ko shakka babu shirin ya samu dimbin nasarori.

A kashi na farko, shirin ya karade Jihohin Kuros Riba, Imo, Kaduna, Kano, Kwara, Ogun da Oyo da kuma Abuja, inda shirin ya bukaci zuba dala biliyan daya a fannin zuba hannun jari na masu zaman kansu, wanda hakan zai taimaka wa manoma wajen rage yin asara a girbin amfanin da suka samu na farko.

Kazalika, Oyelaran ya yi nuni da cewa; samun nasara a zango na daya na shirin ne, zai taimaka a amince da zango na biyu na shirin, wanda kuma ake da yakinin fadada shi a dukkanin daukacin fadin Nijeriya.

Har wa yau, shirin zai taimaka wa Nijeriya wajen samun damammakin amfana da fannin aikin noma da kuma kara bunkasa tattalin arzikinta.

Sai dai, Darakta Janar na bankin na AFDB a Nijeriya, Dakta Abdul Kamara, na da yakinin cewa; wata ganawa da masu ruwa da tsaki a fannin suka yi a kwanakin baya a Abuja, an yi ta ne da nufin sake tattaunawa; domin gaggawar aiwatar da shirin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Italiya

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Italiya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.