ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ba Za Ta Samu Wani Sabon Bashi Daga Bankin AfDB Ba -Farfesa Oyebanji

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
AFDB

Nijeriya za ta yi asarar samun wani sabon bashin a zango na biyu, kan kafa masana’antun noma na shiyya-shiyya (SAPZs).

Kasar za ta yi wannan asara ce, sakamakon jinkirin da aka samu na rashin wanzar da zango na daya na shirin, wanda yawan bashin ya kai kimanin dala miliyan 38.
Babban mai bai wa Shugaban Bankin Raya Nahiyar Afrika (AFDB), Dakta Akinwumi Adesina, Farfesa Oyebanji Oyelaran-Oyeyinka ne ya bayyana hakan.

  • Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano
  • Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Farfesan, ya sanar da hakan ne a lokacin da ya gabatar da wata kasida ta shiri na musamman kan kafa masana’antun noma na shiyya-shiyya a wani taron bita na jihohin da suka amfana da kashin farko na shirin da aka gudanar a A.

ADVERTISEMENT

Ya ce, ma’anar shirin; wata dabara ce ta zamani da za ta taimaka wa Nijeriya wajen fitar da ita daga matsalar rashin aikin yi da kasar ke fuskanta a halin yanzu.

Oyebanji ya kuma yi nuni da cewa, duba da jinkirin da ake fuskanta na wanzar da shirin kashi na daya tare da shirye-shiryen barin ofis na Dakta Akinwumi Adesina, a matsayin shugaban bankin; nan da shekaru biyu, hakan zai sa Nijeriya ta sake neman sake ciwo wani bashin daga bankin.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Har ila yau, ya kuma yi gargadin cewa; matukar Nijeriya ba ta tashi tsaye ba, zai yi wuya ta samu bashin a zango na biyu.
Haka zalika, sai dai wata majiya ta tabbatar da cewa; ba a wanzar da wannan shiri ba, sakamakon guda daga cikin ministocin a wancan lokaci ya soki shirin a wani zama da majalisar zartarwa ta wancan lokacin ta yi.

Amma duk da haka, bayan Dakta Adesina ya zama shugaban bankin AFDB, ya wanzar da shirin; inda bankin ya rika taimaka wa kasashe da dama ciki har da Kasar Ethiopia, wanda ko shakka babu shirin ya samu dimbin nasarori.

A kashi na farko, shirin ya karade Jihohin Kuros Riba, Imo, Kaduna, Kano, Kwara, Ogun da Oyo da kuma Abuja, inda shirin ya bukaci zuba dala biliyan daya a fannin zuba hannun jari na masu zaman kansu, wanda hakan zai taimaka wa manoma wajen rage yin asara a girbin amfanin da suka samu na farko.

Kazalika, Oyelaran ya yi nuni da cewa; samun nasara a zango na daya na shirin ne, zai taimaka a amince da zango na biyu na shirin, wanda kuma ake da yakinin fadada shi a dukkanin daukacin fadin Nijeriya.

Har wa yau, shirin zai taimaka wa Nijeriya wajen samun damammakin amfana da fannin aikin noma da kuma kara bunkasa tattalin arzikinta.

Sai dai, Darakta Janar na bankin na AFDB a Nijeriya, Dakta Abdul Kamara, na da yakinin cewa; wata ganawa da masu ruwa da tsaki a fannin suka yi a kwanakin baya a Abuja, an yi ta ne da nufin sake tattaunawa; domin gaggawar aiwatar da shirin.

AFDB
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
AFDB
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Italiya

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Italiya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.