ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ba Za Ta Samu Wani Sabon Bashi Daga Bankin AfDB Ba -Farfesa Oyebanji

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
AFDB

Nijeriya za ta yi asarar samun wani sabon bashin a zango na biyu, kan kafa masana’antun noma na shiyya-shiyya (SAPZs).

Kasar za ta yi wannan asara ce, sakamakon jinkirin da aka samu na rashin wanzar da zango na daya na shirin, wanda yawan bashin ya kai kimanin dala miliyan 38.
Babban mai bai wa Shugaban Bankin Raya Nahiyar Afrika (AFDB), Dakta Akinwumi Adesina, Farfesa Oyebanji Oyelaran-Oyeyinka ne ya bayyana hakan.

  • Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano
  • Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Farfesan, ya sanar da hakan ne a lokacin da ya gabatar da wata kasida ta shiri na musamman kan kafa masana’antun noma na shiyya-shiyya a wani taron bita na jihohin da suka amfana da kashin farko na shirin da aka gudanar a A.

ADVERTISEMENT

Ya ce, ma’anar shirin; wata dabara ce ta zamani da za ta taimaka wa Nijeriya wajen fitar da ita daga matsalar rashin aikin yi da kasar ke fuskanta a halin yanzu.

Oyebanji ya kuma yi nuni da cewa, duba da jinkirin da ake fuskanta na wanzar da shirin kashi na daya tare da shirye-shiryen barin ofis na Dakta Akinwumi Adesina, a matsayin shugaban bankin; nan da shekaru biyu, hakan zai sa Nijeriya ta sake neman sake ciwo wani bashin daga bankin.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Har ila yau, ya kuma yi gargadin cewa; matukar Nijeriya ba ta tashi tsaye ba, zai yi wuya ta samu bashin a zango na biyu.
Haka zalika, sai dai wata majiya ta tabbatar da cewa; ba a wanzar da wannan shiri ba, sakamakon guda daga cikin ministocin a wancan lokaci ya soki shirin a wani zama da majalisar zartarwa ta wancan lokacin ta yi.

Amma duk da haka, bayan Dakta Adesina ya zama shugaban bankin AFDB, ya wanzar da shirin; inda bankin ya rika taimaka wa kasashe da dama ciki har da Kasar Ethiopia, wanda ko shakka babu shirin ya samu dimbin nasarori.

A kashi na farko, shirin ya karade Jihohin Kuros Riba, Imo, Kaduna, Kano, Kwara, Ogun da Oyo da kuma Abuja, inda shirin ya bukaci zuba dala biliyan daya a fannin zuba hannun jari na masu zaman kansu, wanda hakan zai taimaka wa manoma wajen rage yin asara a girbin amfanin da suka samu na farko.

Kazalika, Oyelaran ya yi nuni da cewa; samun nasara a zango na daya na shirin ne, zai taimaka a amince da zango na biyu na shirin, wanda kuma ake da yakinin fadada shi a dukkanin daukacin fadin Nijeriya.

Har wa yau, shirin zai taimaka wa Nijeriya wajen samun damammakin amfana da fannin aikin noma da kuma kara bunkasa tattalin arzikinta.

Sai dai, Darakta Janar na bankin na AFDB a Nijeriya, Dakta Abdul Kamara, na da yakinin cewa; wata ganawa da masu ruwa da tsaki a fannin suka yi a kwanakin baya a Abuja, an yi ta ne da nufin sake tattaunawa; domin gaggawar aiwatar da shirin.

AFDB
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
AFDB
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Italiya

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Italiya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.