ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ba Za Ta Samu Wani Sabon Bashi Daga Bankin AfDB Ba -Farfesa Oyebanji

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
AFDB

Nijeriya za ta yi asarar samun wani sabon bashin a zango na biyu, kan kafa masana’antun noma na shiyya-shiyya (SAPZs).

Kasar za ta yi wannan asara ce, sakamakon jinkirin da aka samu na rashin wanzar da zango na daya na shirin, wanda yawan bashin ya kai kimanin dala miliyan 38.
Babban mai bai wa Shugaban Bankin Raya Nahiyar Afrika (AFDB), Dakta Akinwumi Adesina, Farfesa Oyebanji Oyelaran-Oyeyinka ne ya bayyana hakan.

  • Rikicin Jam’iyyar NNPP Ya Kazanta A Kano
  • Gwamnan Kano Ya Gabatar Da Kasafin Kuɗin 2025 Na Naira Biliyan 549.1

Farfesan, ya sanar da hakan ne a lokacin da ya gabatar da wata kasida ta shiri na musamman kan kafa masana’antun noma na shiyya-shiyya a wani taron bita na jihohin da suka amfana da kashin farko na shirin da aka gudanar a A.

ADVERTISEMENT

Ya ce, ma’anar shirin; wata dabara ce ta zamani da za ta taimaka wa Nijeriya wajen fitar da ita daga matsalar rashin aikin yi da kasar ke fuskanta a halin yanzu.

Oyebanji ya kuma yi nuni da cewa, duba da jinkirin da ake fuskanta na wanzar da shirin kashi na daya tare da shirye-shiryen barin ofis na Dakta Akinwumi Adesina, a matsayin shugaban bankin; nan da shekaru biyu, hakan zai sa Nijeriya ta sake neman sake ciwo wani bashin daga bankin.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Har ila yau, ya kuma yi gargadin cewa; matukar Nijeriya ba ta tashi tsaye ba, zai yi wuya ta samu bashin a zango na biyu.
Haka zalika, sai dai wata majiya ta tabbatar da cewa; ba a wanzar da wannan shiri ba, sakamakon guda daga cikin ministocin a wancan lokaci ya soki shirin a wani zama da majalisar zartarwa ta wancan lokacin ta yi.

Amma duk da haka, bayan Dakta Adesina ya zama shugaban bankin AFDB, ya wanzar da shirin; inda bankin ya rika taimaka wa kasashe da dama ciki har da Kasar Ethiopia, wanda ko shakka babu shirin ya samu dimbin nasarori.

A kashi na farko, shirin ya karade Jihohin Kuros Riba, Imo, Kaduna, Kano, Kwara, Ogun da Oyo da kuma Abuja, inda shirin ya bukaci zuba dala biliyan daya a fannin zuba hannun jari na masu zaman kansu, wanda hakan zai taimaka wa manoma wajen rage yin asara a girbin amfanin da suka samu na farko.

Kazalika, Oyelaran ya yi nuni da cewa; samun nasara a zango na daya na shirin ne, zai taimaka a amince da zango na biyu na shirin, wanda kuma ake da yakinin fadada shi a dukkanin daukacin fadin Nijeriya.

Har wa yau, shirin zai taimaka wa Nijeriya wajen samun damammakin amfana da fannin aikin noma da kuma kara bunkasa tattalin arzikinta.

Sai dai, Darakta Janar na bankin na AFDB a Nijeriya, Dakta Abdul Kamara, na da yakinin cewa; wata ganawa da masu ruwa da tsaki a fannin suka yi a kwanakin baya a Abuja, an yi ta ne da nufin sake tattaunawa; domin gaggawar aiwatar da shirin.

AFDB
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
AFDB
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai
  • Sulaiman
    Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Italiya

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Italiya

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.