ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu wata Yarjejeniya Da Aka Gindaya Cewa Za A Ba Tinubu Shugaban Kasa Bayan Buhari -Yerima

by Muhammad
4 years ago
Babu

Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Sanata Ahmad Sani Yerima, ya ce babu wata yarjejeniya tsakanin jam’iyyar APC da Ahmad Tinubu, na ba shi takarar shugaban kasar nan bayan mulkin shugaba Muhammadu Buhari.

Yerima, wanda kuma dan takarar shugaban kasa ne a jam’iyyar APC mai mulki, ya bayyana hakan a cikin shirin siyasa na Trust Tv, Daily Politics, a daren Juma’a.

  • Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23
  • 2023: Buhari Zai Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki Don Fitar Da Magajinsa Gabanin Taron APC

Tinubu, yayin da yake zantawa da wakilan jam’iyyar a jihar Ogun a ranar Alhamis, ya ce lokaci ya yi da zai zama shugaban Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan jihar Legas ya kuma bayyana yadda ya goyi bayan Buhari a takararsa ta shugaban kasa tare da ba da ba Osinbajo mukamin mataimakin shugaban kasa, wanda shi ma a halin yanzu ke zawarcin mukamin shugaban kasa bayan ya gama mataimakin shugaban kasa karo na biyu.

Idan zamu iya tunawa, Jam’iyyar Tinubu, (ACN) ta narke wuri guda da sauran Jam’iyyu a watan Fabrairun 2013, tare da (CPC) da (ANPP) – da kuma wani bangare na (APGA) domin kafa jam’iyyar APC tare da Buhari daga jam’iyyar CPC aka ba shi damar tsayawa takarar babban mukami.

LABARAI MASU NASABA

Cikin Sauƙi Na Yanke Shawarar Komawa APC – Gwamna Fubara

Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe

An yi imanin cewa akwai yarjejeniyar da ACN ta yi na cewa za ta fitar da dan takarar shugaban kasa na gaba bayan mulkin Buhari.

Sai dai Yerima ya ce babu wani rahoto da ke nuna an kulla irin wannan yarjejeniya da jam’iyyar.

“Babu wata yarjejeniya da t tabbatar da haka, a lokacin wanene shugaban jam’iyyar? Da farko muna da Cif Bisi Akande, daga baya kuma, muna da John Oyegun, kuma a yau muna da Sanata Abdullahi Adamu, muna da [Mai Mala] Buni a cikin tafiyar da dai sauransu.

“To, ko Cif Bisi Akande ne ya zauna da wasu mutane? Duk wani hukunci da aka dauka a wajen tsarin jam’iyyar ba a amince da shi ba. Jam’iyyar tana da kwamitin ayyuka na kasa, jam’iyyar kuma tana da abin da muke kira NEC kuma akwai bangaren yanke shawara gaba daya wato babban taron kasa.

Ya ci gaba da cewa, “Duk hukuncin da ba a dauka a cikin tsarin jam’iyyar ba, ba hukunci ba ne. Ba za ku iya samun fahimta da mutum ba kuma ku ce ‘hakan zai faru. Idan jam’iyya tana son yanke shawara, ko dai kwamitin ayyuka na kasa ne, ko hukumar zabe ta yanke.

“Idan Yarjejeniyar ta yanke shawara, ba za a iya canza ta ba. Amma za a iya sake duba yanke shawara bisa kowane yanayi. Ko da akwai wannan fahimtar, yanayin yau na iya bambanta da yadda yake lokacin da aka cimma wannan fahimtar. ”

Jam’iyyar APC ta tsayar da ranar 6 ga watan Yuni a matsayin ranar babban taronta a birnin tarayya Abuja, inda za ta zabi dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Siyasa

Cikin Sauƙi Na Yanke Shawarar Komawa APC – Gwamna Fubara

December 18, 2025
Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe
Siyasa

Ba Zan Taɓa Komawa Jam’iyyar APC Ba — Abaribe

December 16, 2025
El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027
Siyasa

El-Rufai Ya Ƙaryata Rahoton Goyon Bayan Yanki Ko Wani Mutum A Zaɓen 2027

December 15, 2025
Next Post
Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

Mene Ne Bambancin Wadannan Ruwan Guda Biyu Masu Fitowa Daga Gaban Mace?

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.