• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

by Idris Aliyu Daudawa
6 months ago
in Ilimi
0
Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar Litinin ce mataimakin shugaban jami’ar Ajayi, Farfesa Timothy Adebayo Timothy Adebayo, ya ce babbar matsalar da take damun ilimi a Nijeriya ita ce rashin isassun kudaden da za’a tafiyar da shi ilimin.

Adebayo ya bayyana hakan ne lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen taro lokacin da aka yi bikin yaye dalibai na Jami’ar  na 16 a Oyo Jihar Oyo.

  • Jami’in Yada Labarai: Kasar Sin A Shirye Take Ta Aiwatar Da Hadin Gwiwar Kasashe Na Hakika Tare Da Mambobin G20
  • Jami’i: Kofar Sin A Bude Take Domin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa Da Amurka Don Inganta Dangantakar Tattalin Arziki Mai Daidaito

Ya ce matslar bata tsaya kadai bane kan Jami’oi masu zaman kansu, saboda akwai na Jiha da gwamnatin tarayya, da suke kara kudaden karatu saboda hakan ne zai taimaka musu tafiyar da harkokinsu da suka shafi kudade.

Ya kara jaddada cewa, “Rashin samun damar isassun kudade hakan yana nufin yawan manyan makarantu da kyar suke samar da abubuwan da suka zama dole na dakin gwaji, da sauarn wasu abubuwan more rayuwa da ake bukata saboda  bunkasar ilimi a Nijeriiya.

“Kana iya magana kan gidauniyar tallafawa manyan makarantu na amince ta taimakawa ilimi kwarai da gaske,sai dai kuma siyasar da take tattare da yadda take fitarwa da bada kudade, hakan bai sa gidauniyar ta yi wani abin azo a gani ba a bangaren ilimi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

“Ba abin mamaki bane yadda Jami’oi masu zaman kansu suke kara kudin makaranata kai har ma na gwamnatoci suna kara kudaden, duk kuwa da yake akwai hukumar ko gidauniyar TETFUND bada taimako kawai saboda su yi bayani yadda suke kashe kudaden, wannan ya nuna yadda irin Jami’oin suke ta fadi- tashi kan lamarin da ya shafi kudi.”

Mataimakain shugaban jami’ar ya ce ACU ta samu ci gaba ta bangaren ilimi da kuma yadda take a shekarun baya da suka wuce,inda ya bayyana cewa jami’ar gaba take  da fara yin tsarin karatu a gida.

“Jami’ar tana yin duk abubuwan da za ta iya domin ta samu damar bullo da cibiyar tsarin karatu a gida ODL domin ta kara samar da hanyoyin da wasu mutane wadanda ke fuskantar matsala wajen samun damar  zuwa manyan makarantu domin kara ilimi kamar yadda ya jaddada’’.

Da yake bayan ikan ire- iren abubuwan karatun daya samar  a shekaru hudu da suka gabata ga wadanda ya tarad , Adebayo ya ce  an kara samar da kayayyaki aiki 29, yayin da kuma Jmi’ar ta  fara tsarin musayar dalibai da makarantu 15 a cikin gida da kuma wajen Nijeriya.

Daga karshe ya ce za’a b awasu mutane,2,679 takardun shedar kammala Jami’a a bikin yaye dalibai na wannan shekarar inda 86 suka samu digiri mai daraja ta daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jama'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwarzon Ɗan Siyasar Shekarar 2024: Adams Oshiomhole (CON)

Next Post

Bauchi Ta Ba Ma’aikatar Ilimi Muhimmanci A Kasafin Kudin 2025

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

6 days ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Ilimi

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

7 days ago
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
Ilimi

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

7 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

7 days ago
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
Ilimi

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

2 weeks ago
Next Post
Bauchi Ta Ba Ma’aikatar Ilimi Muhimmanci A Kasafin Kudin 2025

Bauchi Ta Ba Ma’aikatar Ilimi Muhimmanci A Kasafin Kudin 2025

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.