ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Ajayi Crowther Ta Bayyana Matsalolin Da Ta Ke Fuskanta Wajen Gudanar Da Harkokinta

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Jami'ar

Ranar Litinin ce mataimakin shugaban jami’ar Ajayi, Farfesa Timothy Adebayo Timothy Adebayo, ya ce babbar matsalar da take damun ilimi a Nijeriya ita ce rashin isassun kudaden da za’a tafiyar da shi ilimin.

Adebayo ya bayyana hakan ne lokacin da yake gabatar da jawabi a wajen taro lokacin da aka yi bikin yaye dalibai na Jami’ar  na 16 a Oyo Jihar Oyo.

  • Jami’in Yada Labarai: Kasar Sin A Shirye Take Ta Aiwatar Da Hadin Gwiwar Kasashe Na Hakika Tare Da Mambobin G20
  • Jami’i: Kofar Sin A Bude Take Domin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa Da Amurka Don Inganta Dangantakar Tattalin Arziki Mai Daidaito

Ya ce matslar bata tsaya kadai bane kan Jami’oi masu zaman kansu, saboda akwai na Jiha da gwamnatin tarayya, da suke kara kudaden karatu saboda hakan ne zai taimaka musu tafiyar da harkokinsu da suka shafi kudade.

ADVERTISEMENT

Ya kara jaddada cewa, “Rashin samun damar isassun kudade hakan yana nufin yawan manyan makarantu da kyar suke samar da abubuwan da suka zama dole na dakin gwaji, da sauarn wasu abubuwan more rayuwa da ake bukata saboda  bunkasar ilimi a Nijeriiya.

“Kana iya magana kan gidauniyar tallafawa manyan makarantu na amince ta taimakawa ilimi kwarai da gaske,sai dai kuma siyasar da take tattare da yadda take fitarwa da bada kudade, hakan bai sa gidauniyar ta yi wani abin azo a gani ba a bangaren ilimi.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

“Ba abin mamaki bane yadda Jami’oi masu zaman kansu suke kara kudin makaranata kai har ma na gwamnatoci suna kara kudaden, duk kuwa da yake akwai hukumar ko gidauniyar TETFUND bada taimako kawai saboda su yi bayani yadda suke kashe kudaden, wannan ya nuna yadda irin Jami’oin suke ta fadi- tashi kan lamarin da ya shafi kudi.”

Mataimakain shugaban jami’ar ya ce ACU ta samu ci gaba ta bangaren ilimi da kuma yadda take a shekarun baya da suka wuce,inda ya bayyana cewa jami’ar gaba take  da fara yin tsarin karatu a gida.

“Jami’ar tana yin duk abubuwan da za ta iya domin ta samu damar bullo da cibiyar tsarin karatu a gida ODL domin ta kara samar da hanyoyin da wasu mutane wadanda ke fuskantar matsala wajen samun damar  zuwa manyan makarantu domin kara ilimi kamar yadda ya jaddada’’.

Da yake bayan ikan ire- iren abubuwan karatun daya samar  a shekaru hudu da suka gabata ga wadanda ya tarad , Adebayo ya ce  an kara samar da kayayyaki aiki 29, yayin da kuma Jmi’ar ta  fara tsarin musayar dalibai da makarantu 15 a cikin gida da kuma wajen Nijeriya.

Daga karshe ya ce za’a b awasu mutane,2,679 takardun shedar kammala Jami’a a bikin yaye dalibai na wannan shekarar inda 86 suka samu digiri mai daraja ta daya.

Jami'ar
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Bauchi Ta Ba Ma’aikatar Ilimi Muhimmanci A Kasafin Kudin 2025

Bauchi Ta Ba Ma’aikatar Ilimi Muhimmanci A Kasafin Kudin 2025

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Sabon Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Tattaunawa Da Wakilan ‘Yan Kasuwa Mahalarta Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na DAVOS

June 25, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.