ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗangote Ne Gwarzon Jaridar LEADERSHIP Na Shekara Ta 2024

by Leadership Hausa
1 year ago
dangote

Alhaji Aliko Dangote, wanda aka fi sani da babban ɗan kasuwa kuma wanda ya fi kowa arziki a Afrika, ya zama wata alama da ke nuna ci gaba da bunƙasar tattalin arziƙi a nahiyar.

Dangote ya kasance ginshiƙi wajen kawo sauye-sauye a fannin masana’antu da rage dogaro da shigo da kayayyaki, a ƙoƙarinsan na tabbatar da wadatar kayan masarufi a cikin gida. Wannan karramawa ta Gwarzon Shekara ta 2024 ta tabbatar da irin tasirinsa a harkar masana’antu, da ci gaban al’umma, da kyautata rayuwar jama’a a duk faɗin Afrika.

  • Dangote Ya Rage Wa ‘Yan Kasuwa Farashin Man Fetur
  • Matatar Dangote Ta Fara Fitar Man Fetur Dinta Zuwa Kasashen Afrika

Tarihi da Farko na Rayuwa

ADVERTISEMENT

An haifi Aliko Dangote a Kano, Nijeriya, cikin iyali masu rikon gaskiya da goge wa a kasuwanci. Kakansa, Alhaji Sanusi Dantata, ya kasance ɗaya daga cikin manyan attajirai a Afrika ta Yamma, wanda ya kafa babban kamfani na cinikin gyada. Wannan tarihi na kasuwanci ya tasirantu ga Dangote tun yana ƙarami, inda ya nuna sha’awar shiga kasuwanci tun yana makarantar firamare.

Karatu da fara Kasuwancinsa

LABARAI MASU NASABA

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Dangote ya yi karatu a Jami’ar Al-Azhar, Cairo, ƙasar Masar, inda ya samu digiri a fannin kasuwanci. Bayan dawowa Nijeriya a 1978, ya samu bashin Naira 500,000 daga ƙanin mahaifinsa, Alhaji Sanusi Dantata. Wannan rance ya ba shi damar fara kasuwancin kayayyaki kamar siminti, da shinkafa, da sukari, da shinkafa, tare da mayar da hankali kan buƙatun jama’a da kuma rage giɓin kayan masarufi a cikin gida.

A yayin gudanar da kasuwancin sayar da kayan masarufi, Dangote ya fahimci cewa dogaro da shigo da kaya daga ƙasashen waje na kawo cikas ga haɓakar tattalin arziki. Ya yi tambayoyi masu muhimmanci kamar: “Me ya sa za a ke shigo da sukari idan za a iya samar da shi cikin gida?” Wannan tunanin ya sa ya koma masana’antu, inda ya kafa kamfanoni da suka shafi sukari, da gishiri, da siminti. Wannan mataki ya zama ginshiƙin arziƙinsa kuma ya sauya za yanayin masana’antu a Nijeriya da Afirka baki ɗaya.

Masana’antu

Kamfanin Simintin Dangote ya zama babbar masana’antar siminti a Afrika, yana samar da kayan gini da suka rage dogaro da shigo da kaya. Wannan nasarar ta tabbatar da matsayin Dangote a matsayin jagora a harkar masana’antu. Bugu da ƙari, ya ƙaddamar da shirin samar da sukari da man fetur, wanda ya ƙara wa tattalin arzikin Nijeri ya ƙarfin gwiwa.

Matatar Dangote

Matatar Dangote, wadda ke Legas, ta zama babban ginshiƙi a harkar makamashi a Afirka. Wannan masana’anta mai iya sarrafa ganga 650,000 na mai a kowace rana, tana rage dogaro da shigo da mai daga ƙasashen waje. An kaddamar da masana’antar a watan Mayu na 2023, kuma ta fara samar da dizal da man jirgin sama a farkon 2024.

Haka kuma, wannan masana’antar ta fara samar da Fetur (Premium Motor Spirit (PMS) a watan Satumba 2024, wanda ya kawo sauyi mai girma wajen rage shigo da man fetur. Matatar Dangote ta taimaka wajen rage asarar kuɗaɗe ta hanyar kawar da buƙatar shigo da man fetur daga ƙasashen waje, tana ceton Nijeriya kimanin dala biliyan 7.32 a duk shekara.

 

Gudummawar A Fannin Tattalin Arziki Da Samar Da Aiyuka

Dangote ya zuba jarin sama da dala biliyan 25 a fannonin masana’antu, wanda ya haifar da damar samun aiki ga miliyoyin mutane. Masana’antu kamar kamfanin Simintin Dangote, da na Sukari Dangote, da Matatar Dangote sun kasance ginshiƙi wajen rage rashin aikin yi da kuma haɓaka tattalin arziki a Nijeriya da sauran ƙasashen Afirka.

 

Kyautata Rayuwa

Ta hanyar Gidauniyar Aliko Dangote Foundation (ADF), Dangote ya ba da tallafi ga fannonin kiwon lafiya, da ilimi, da rage talauci. An kafa wannan gidauniya a 1994, sannan aka sake mata suna zuwa Aliko Dangote Foundation a 2018. Gidauniyar ta fi mayar da hankali kan magance rashin abinci mai gina jiki, yaki da cututtuka kamar na annobar irinsu polio, da Ebola, da COVID-19, da kuma bayar da tallafi ga waɗanda bala’o’i suka shafa kamar ambaliya.

 

Nasara da Lambar Yabo

A 2008, Dangote ya fara bayyana a jerin masu arziƙi na mujallar Forbes, kuma tun daga nan ya kasance mai tasiri a duniya. A 2011, ya zama mutum na farko a jerin attajirai 40 na Afrika. Haka kuma, ya sami lambobin yabo daban-daban, ciki har da GCON daga gwamnatin Nijeriya a 2011, Grand Commander of the National Order of the Republic of Benin (2013), da Commander of the National Order of Valour na Kamaru (2021).

 

Jagoranci a Kasuwanci

A matsayin shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote ya tabbatar da cewa jagoranci na gaskiya da hangen nesa zai iya kawo ci gaba mai ɗorewa. Rukunin kamfanonin Dangote na aiki a ƙasashe 17 na Afrika, hakan yana tabbatar da cewa yana taimakawa wajen bunƙasa masana’antu da tattalin arziƙin nahiyar baki ɗaya.

 

Halayen Jagoranci Da Mutunci

An san Dangote da sauƙin kai, da riƙon amana, da jajircewa wajen ganin Afrika ta zama mai dogaro da kai. Salon jagorancinsa ya sa kamfanoninsa suka zama abin koyi a duniya.

 

Tasiri Mai Dorewa

A yau, Dangote ya kafa tarihi a harkar masana’antu da tattalin arziƙi. Ya zama gwarzon da ya bunƙasa masana’antu a Afrika, ya mai da hankali kan rage talauci da kuma haɓaka rayuwar jama’a. Wannan lambar yabo ta Gwarzon Shekara ta 2024 ta tabbatar da irin rawar da ya taka wajen sauya yanayin tattalin arziƙin Afrika, tare da zama abin koyi ga shugabanni da ƴan kasuwa masu tasowa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa
Labarai

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli
Labarai

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Next Post
Amfanin Atisaye Ga Mai Juna-biyu

Amfanin Atisaye Ga Mai Juna-biyu

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.