• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Wata Sana’a Da Take Da Daukaka Da Samu Irin Harkar Fim – Hajara Usman 

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
6 months ago
in Nishadi
0
Babu Wata Sana’a Da Take Da Daukaka Da Samu Irin Harkar Fim – Hajara Usman 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin dattawa mata a masana’antar Kannywood wadanda su ka dade ana damawa dasu kuma har yanzu suke haskakawa a masana’antar, a wata hira da aka yi da ita a dandalin Hadiza Gabon mai suna Gabon’s Room Talk Show ta bayyana cewar babu wata sana’a da ake samun daukaka da samun alheri kamar sana’ar fim.

Hajara Usman ko kuma Mama Hajo kamar yadda wasu ke kiranta ta tabbatar da cewar sana’ar fim ba sana’a ce karama ko kuma wadda ta kunshi nishadi kawai kamar yadda wasu ke kallo ba, sana’a ce babba da ya kamata duk wani wanda ya ke kika da niyyar shigowa cikinta ya tabbatar ya dauke ta da muhimmanci domin shima ya samu tarin alherin da yake a cikinta.

  • Allah Ya Yi Wa Mawaƙin Kannywood, El-Mu’az Birniwa Rasuwa
  • Tun Kafin A Samu Masana’antar Kannywood Nake Harkar Fim – Lilisco

Ina bayar da shawara ga yara da manya da ke da sha’awar shiga harkar fim da su tabbatar da cewar sun shigo da niyya daya, kuma su dauketa da muhimmanci sosai domin kuwa harka ce mai kyau ba yadda wasu ke daukatarta ba, wasu sun dauka cewar kawai ka fito a fim a kalleka idan ka tafi wajen taro yara su dinga ihu su na binka shi ne fim,wanda ko kusa wannan ba haka yake ba in ji Mama Hajara wadda ta shafe shekaru fiye da 20 ana damawa da ita a masana’antar.

Tunda farko dai ta bayyana cewar wannan masana’antar ta Kannywood ta yi mata komai a rayuwa domin kuwa duk wani abin alheri da sana’a za ta iya yi wa mutum to tabbas ta samu a wannan harka,saboda haka babu abinda za ta ce a kan wannan sai hamdala ga Allah madaukakin Sarki.

Dangane da yadda wasu manya a masana’antar ke dauka cewa ba su samun girmamawar da ta dace daga kananan jarumai a masana’antar, Hajara Usman ta ce a nata bangaren ba haka abin yake ba domin kuwa mata da maza a masana’antar Kannywood na matukar ganin girmanta kuma har gobe tana da kima a idonsu,don kuwa babu wani abu na raini da ya taba shiga tsakaninta da matasan jarumai.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

A kan yadda wasu dattawa a masana’antar har wayau ke ganin basu samun daidaito wajen biyan kudin aiki duba da cewar sun tsufa ana ganin kamar matasa sun fi dacewa da a biya su kudade masu yawa,Mama Hajo ta ce duk wanda yake da irin wannan tunanin to ba a matsayin sana’a ya dauki harkar fim ba, don kuwa inda a matsayin sana’a ya dauki fim da ba zai yi wannan batun ba.

Ni a tunanina duk wanda ya dauki kudi ya baka a matsayin kudin sallama to ya na ganin su ne suka dace da kai, kuma ai sana’a ‘yar yau da gobe ce idan yau ka yi wa wannan aiki ya biyaka kadan gobe wancan zai biyaka da yawa idan ka yi mashi aiki, saboda haka ba na daukar wannan a matsayin wata matsala don kuwa kowane allazi da nashi amanu in ji ta.

Daga karshe ta yi karin haske dangane da yadda masana’antar Kannywood ta ke a lokacin baya da kuma yanzu inda ta ce a baya duk wanda ya yi fim zai dauka ya kai kasuwa ya siyar wa mutane, musamman wadanda suke zaune a karkara za su saye su kalla a gidajensu ko gidajen kallo da ake budewa a kauyuka, amma yanzu da ake dora fina finai a shafukan yanar gizo muddin ba babbar waya ka mallaka ba,ba lallai ne ka iya kallon sabon fim ba.

Saboda haka ta ce a nata tunanin da za a ci gaba da amfani da duka hanyoyin kallo ma’ana faifan cd da shafukan yanar gizo da abin zai fi,wanda zai iya kalla a faifan cd ya kalla haka zalika wanda zai tafi shafukan yanar gizo ya kalla shima sai ya kalla ba tareda wata matsala ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalar Tsaro: Matawalle Ya Ziyarci Jihar Zamfara

Next Post

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Ingiza Ukraine Ta Takali Fada

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

3 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Ingiza Ukraine Ta Takali Fada

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Ingiza Ukraine Ta Takali Fada

LABARAI MASU NASABA

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.