ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

by Sadiq
1 year ago
Nasarawa

Rundunar ‘yansandan Jihar Nasarawa, ta hana wasu mutane biyu shigo da manyan makamai cikin jihar. 

An kama su ne da misalin ƙarfe 3 na daren ranar 4 ga watan Yuni, 2025 a garin Lafia.

  • Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
  • Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Kakakin ‘yansandan jihar, SP Ramhan Nansel, ya bayyana cewa bayan samun sahihin bayani, rundunar ta aike da jami’anta daga sashen yaƙi da garkuwa da mutane, inda suka cafke mutanen.

ADVERTISEMENT

Ana zargin su da niyyar kai makaman zuwa Ilorin, babban birnin Jihar Kwara.

Mutanen da aka kama su ne Lawal Sani, mai shekaru 40, direban mota daga ƙaramar hukumar Funtua a Jihar Katsina da kuma Dahiru Abdullahi, mai shekaru 75, dillalin shanu daga unguwar Angwan Dosa a Kaduna ta Arewa a Jihar Kaduna, wanda ɗan kasuwar shanu ne a Keffi da ke Nasarawa.

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

An kama su da manyan makamai ciki har da bindiga ƙirar GPMG, bindigu ƙirar AK-47 da sauransu.

Mutanen sun amsa laifin da ake zargin su, inda suka ce an biyasu Naira 500,000 domin su kai makaman daga Jihar Binuwsi zuwa Kwara.

Rundunar ‘yansandan ta ce da ba a kama su ba, makaman na iya shiga hannun ‘yan ta’adda.

Ana ci gaba da bincike domin gano sauran mutanen da ke da hannu a wannan harkar safarar makamai.

Kwamishinan ‘yansandan, ya ce Nasarawa ba mafaka ba ce ga masu laifi, kuma za su ci gaba da yaƙi da masu safarar makamai ba bisa ƙa’ida ba.

Ya kuma roƙi jama’a da su riƙa sanar da duk wani abin da suka gani mai kama da laifi, inda ya bayyana layukan gaggawa da za a iya kiran su: 08112692680, 08032564469, 08036157659, 08037461715, da 07032532391.

MASU ALAKA

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi
Rahotonni

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

June 5, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike
Labarai

Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

June 5, 2026
Next Post
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

June 5, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

June 5, 2026
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

June 5, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

June 5, 2026
Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

June 5, 2026
Shugaban Kasar Laos: Layin Dogo Na Sin Da Laos Ya Sa Burin Al’Ummar Laos Ya Zama Gaskiya

Shugaban Kasar Laos: Layin Dogo Na Sin Da Laos Ya Sa Burin Al’Ummar Laos Ya Zama Gaskiya

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.