ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

by Rabi'at Sidi Bala
1 year ago
Kannywood

Atatullahi Tage daya daga cikin jarumai a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood a wata hira da yayi da jaridar DCL Hausa a cikin shirinsu na sirrin daukaka ya tabo batutuwa da dama da suka shafi masana’antar ciki har da abin da ya kira shamaki ga ci gaban wannan babbar masana’anta da dubban al’umma ke neman abinci a cikinta.

Ni dai an haife ni a jihar Jigawa wanda cikin ikon Allah zama ya dawo dani nan Kano, sakamakon mahaifina da yake zaune a nan tsawon lokaci, abubuwa da dama sun sa ban yi zurfi a karatun zamani ba domin kuwa ko makarantar Sakandire ban kammala ba ko da na bar zuwa makaranta in ji Ayatullahi.

  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi

A lokacin da na zo Kano na yi sana’oi da dama kafin in zama abin da na zama a yanzu kama daga tallar kaset a baro, inda nike zuba kaset-kaset a baro ina zagayawa ina sayarwa, daga wannan sana’a ce na dawo harkar fim gadan-gadan, a wancan lokacin ban gamu da wani cikas yayin shigata harkar fim ba kamar yadda nike ji wasu na fadin matsalolin da suka fuskanata yayin shigiwa.

ADVERTISEMENT

Dalili kuwa shi ne ko da na fara wannan harka ta fim bani da wani wanda ke tsawatar mani sakamakon iyayena da suka rasu, a wancan lokacin ma ba kowa ne ya damu da abin da na samu ko ya sameni ba, wasu mutane ma kallon wani mutum marar amfani suke yi mani, da haka dai na ci gaba da dagewa har Allah ya kawo ni inda nike yanzu ya kara da cewa.

Da yake amsa tambaya akan minene sirrin samun daukakarshi Tage ya ce ba komai ba ne sirrin samun daukaka illa Hakuri, Biyayya da kuma aiki tukuru, domin kuwa idan ka saka wadanann a zuciyarka to komai zai zo maka a cikin sauki ba tare da ka wahala ba, yanzu sau da dama mutane sun fi son su samu abu cikin sauki kuma cikin lokaci ba tare da sun wahala ba.

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

Sai kaga mutum daga ya samu wata yar dama to do yake ace ya samu wata hanyar wulakanta wannan wanda yayi masa rana kokuma ya wuce shi a matsayi ko wani abin Duniya ba tareda la’akari da cewar wannna wanda ya koya maka to ya fika sanin komai a wannan harkar musamman ma a nan masana’antar Kannywood.

Don haka kamata ya yi ce mutane sun fahimci cewar babu ta yadda za a yi ka ci gaba matukar ka na da wata niyyar cin amanar wanda ya taimake ka ka kai wani matsayi na rayuwa, ni yanzu a matsayina na Ayatullahi Tage na yi biyayya ga maigidana Alhaji Tage wanda ya nuna mani hanya, ya rike ni kamar dan da ya haifa, kuma yake fatan duk wani alheri na Duniya ya same ni.

Ga shi yanzu ina ganin amfanin biyayyar domin kuwa duk wani abin da ake fatan samu na alheri a wannan masana’antar Allah ya nufe ni da samu kama daga mutunci, daukaka da kuma abin Duniya, don haka nike shawartar ‘yan uwa abokan sana’ara da ma sauran mutane da su kasance masu biyayya a duk inda suka samu kansu a rayuwa kuma kada su zamo masu girman kai ko nuna kyashi ga abin da wani ya samu domin kuwa  Allah mai iko ne akan kowa da komai zai iya baiwa wanda bai da shi, ya kuma amshe ga wanda ke da shi idan yaga dama.

Dangane da matsaloli ko kalubale da masana’antar Kannywood ke fuskanta Tage ya ce, ba komai ya janyo hakan ba illa rashin hadin kai a tsakanin masana’antar, duk al’ummar da aka ce babu hadin kai a tsakaninsu to lallai za ka samu wannan al’umma babu wani cigaba da suka samu, to amma matukar muka hada kanmu ya zamana mun zamo tsintsiya madaurinki daya babu wata baraka da za ta iya shigowa a cikinmu ya tabbatar.

Muddin aka ce akwai hassada ko kyashi a tsakaninmu to zai yi wuya mu dinga bai wa junanmu shawarwarin da za su ciyar da masana’antar gaba, sakamakon haka kuwa ba karamar illa zai janyo mana ba, don haka nike kira ga mahukunta da sauran al’umma da ke cikin Kannywood da mu daure mu hada kanmu domin mu kai wannan masana’antar inda ya kamata ta kasance.

Daga karshe ya bukaci mutane da ke furta kalaman tsinuwa ga jaruman fim da suji tsoron Allah su bari, idan kuma ba haka ba to su sani cewa su kansu basu san wadanda za su haifa ba, mai yiwuwa su haifi yaron da zai ji ya na sha’awar  harkar fim kuma ya shigo harkar a dama dashi, to idan haka ta faru wannan tsinuwar da sukayi wa jaruman fim za ta shafi yayansu da suma suka shiga cikin harkar fim din.

Kannywood
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.