• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jagoranci Nagari: Kungiyar Lauyoyi Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Jagoranci Nagari: Kungiyar Lauyoyi Ta Karrama Gwamnan Zamfara Da Lambar Yabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada cewa tabbatar da doka da oda na buƙatar ƙwarewa ta fasaha, jajircewa da kuma gaskiya da riƙon amana.

 

Gwamna Lawal ya kasance babban baƙo a wajen taron shari’a na shekara-shekara ta 2024 da Ƙungiyar Lauyoyi ta Ƙasa (NBA) reshen Gusau ta shirya.

  • Saudiyya Ta Ware Dala Biliyan 100 Don Sabunta Masallatan Harami
  • Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa a yayin taron, gwamna Lawal ya samu lambar yabo ta karramawa a matsayin babban abin tunawa kuma mutum mai tasiri ga al’ummar jihar Zamfara.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

Ya ƙara da cewa, shugaban NBA reshen Gusau Mu’azu Shehu Ahmad Esq ne ya ba gwamnan lambar yabon.

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya sake nanata cewa taro kamar na NBA yana ƙara ƙwarin gwiwa ga ƙwararrun lauya don musayar ra’ayoyi da inganta samar da adalci, dimokuraɗiyya, da bin doka.

 

Ya ce, “Taken taron na bana shi ne; “Tabbatar da Doka: Ginshiƙin Ci gaban Dimokraɗiyya”. Yana nuna da irin rawar da fannin shari’a ke takawa wajen tsara al’ummarmu ta hanyar tabbatar da kyawawan ɗabi’u, adalci da riƙon amana.

 

“Ina da yaƙinin cewa za mu iya ƙarfafa ginshiƙin dimokuraɗiyyar mu da kuma ginshiƙin wanzuwar mu a matsayin al’umma ta hanyar sadaukar da kai ga bin doka da oda.

 

“A halin da ake ciki, ina yaba wa Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya reshen Gusau, bisa namijin ƙoƙarin da suke yi na tabbatar da adalci da bin doka da oda. Haƙiƙa sadaukarwar da kuka yi ga wannan aiki mai daraja abin a yaba ne kuma abin koyi ne.

 

“Ina kira gare ku da ku ci gaba da nuan halin ƙwarai na ma’aikatan shari’a don tabbatar da cewa kun kasance ginshiƙin fata ga talakawa da duk masu neman adalci.

 

“Na yaba wa ƙoƙarin lauyoyi wajen ganin an yi adalci ba tare da nuna son kai ba cikin gaggawa, har a lokutan da ake fuskantar ƙalubale. Tsayuwarku ta kasance ƙwarin gwiwa kuma ta zama abin tunatarwa cewa adalci shi ne ginshiƙin kowace al’umma mai wayewa.

 

“Gwamnatin jihar Zamfara ta tsaya tsayin daka wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali. Muna aiki tuƙuru don magance matsalolin rashin tsaro da samar da yanayin da al’ummarmu za su zauna ba tare da tsoro ba.

 

“Ina kuma so in jaddada muhimmancin ilimin shari’a wajen ƙarfafa tsarin adalcinmu.

 

“Tsarin ilimin shari’a yana buƙatar karatu da haƙiƙa. Ina roƙon ku da ku riƙa amfanar juna wajen da horo da ilimin da ku ka samu, kamar wannan taro na makon shari’a, don kasancewa a sahun gaba wajen aiki da doka.

 

“A wannan lokaci, ina miƙa godiya ta ga waɗanda suka shirya wannan babbar lambar yabo a gare ni. Jajircewar da na yi na yaƙar rashin tsaro, da bin doka da oda, da gina ababen more rayuwa abin a yaba ne matuƙa.

 

“Ba abin alfahari ba ne kawai, a’a, shaida ce ga namijin ƙoƙarin da duk waɗanda suka yi aiki tare da ni suka yi wajen gina jihar Zamfara mai tsaro, da adalci, da wadata cikin watanni 20 da suka gabata.

 

“A ƙarshe, yayin da nake yaba wa Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya reshen Gusau, kan yadda suka saba shirya wannan taron na shekara-shekara, cikin alfahari nake bayyana buɗe makon taron shari’a na 2024. Ina addu’ar shawarwarinku su kasance masu ma’ana da tasiri. Allah Ta’ala Ya yi mana jagora a cikin ayyukanmu baki ɗaya”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DSS Ta Maka Mahdi Shehu A Kotu Kan Zargin Ta’addanci

Next Post

Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

Related

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

27 minutes ago
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

2 hours ago
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu
Manyan Labarai

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

3 hours ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

4 hours ago
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja
Kiwon Lafiya

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

6 hours ago
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida
Manyan Labarai

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

7 hours ago
Next Post
Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.