ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Albishir Ga Masu Kawo Ziyara Ko Yada Zango A Birnin Beijing Na Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Biranen kasar Sin na gudanar da gyare-gyare na ci gaban zamani a bangaren kyautata jin dadin baki masu kawo ziyara ko kuma yada zango. Inda hakan ke haifar da kyakkyawan sakamako daga irin tsokacin da baki ke yi kan sabbin tsare-tsaren da suka gani a biranen.

Wasu ‘yan uwa su biyu daga Poland da suka kawo ziyarar kwanaki hudu a birnin Beijing kwanan baya, sun bayyana cewa, kasar Sin ta burge su sosai, bisa yadda suka ga an ci gaba da raya manyan biranen kasar tare da saukaka mu’amalar biyan bukatun masu yawon bude ido na kasashen waje.

  • Kasar Sin Ta Mallaki Tashoshin Sadarwar 5G Miliyan 4.25
  • Borrusia Dortmund Ta Sallami Kocinta, Nuri Sahin

Dagmara Paszkowska, wacce ta ziyarci kasar Sin tare da dan uwanta Norbert ta ce, “Mun lura za mu iya biyan kudin hidindimu ko abubuwan da muka saya ta hanyar amfani da tsabar kudi, ko kati, ko kuma ta hanyar tambarin QR, kana mun yi mamakin cewa ana ma iya amfani da hanyar tantance fuska wajen biyan kudi.”

ADVERTISEMENT

A wani bangare na sabon tsarin biyan kudi da tafiye-tafiye da aka kaddamar a ranar 1 ga Janairun nan don saukaka mu’amaloli ga baki, an samar da wuraren tuntuba don neman biyan bukata ta kusurwowin da bakin za su yi kacibis da su da zarar sun iso manyan filayen jiragen sama guda biyu na Beijing, wato na Beijing Capital da na Beijing Daxing.

Kaddamar da wadannan wurare da birnin Beijing ya yi a manyan tasoshinsa na jiragen sama ta zo a kan gaba, a daidai da lokacin da ake samun karuwar baki daga kasashen waje sakamakon fadada manufofin kasar Sin na shigowa ba tare da biza ba ga matafiya daga kasashe 54, da kuma damar shiga kai-tsaye ga baki masu fasfo daga kasashe 38 da ke bukatar gajeren zama a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

A halin yanzu, kusan a kullum, ana samun baki ‘yan kasashen waje 252 de ke shiga birnin Beijing tare da takardar izinin shiga ta wucin-gadi ta sa’o’i 240 wacce aka kara mata wa’adi daga sa’o’i 144, kamar yadda mataimakin shugaban sashen musayar waje da hadin gwiwa na ofishin al’adu da yawon bude ido na birnin Beijing, Wang Hongyan, ya tabbatar a wani taron manema labarai.

A shekarar 2024, birnin Beijing ya sami ziyarce-ziyarce miliyan 3.94, wadanda suka karu da kashi 186.8 cikin dari a mizanin shekara-shekara, inda hakan ya kara yawan kudin shiga na yawon bude ido na birnin da kashi 151.7 cikin dari, watau zuwa dala biliyan 4.91, kuma mahukuntan da abin ya shafa sun lashi takobin kara kyautata jin dadin baki masu ziyara ta hanyar inganta tsare-tsaren yawon bude ido, masaukai da sayayya da hanyoyin biyan kudi masu gamsarwa.

Tsarin amfani da katin komai-da-ruwanka na “Beijing Pass” na daga cikin abubuwan da ke saukaka mu’amalar baki a birnin ta yadda wadanda suka saye shi ba kawai za su iya amfani da shi wajen biyan kudin sufuri a cikin birane 300 na kasar Sin ba ne, har ma za su iya shiga wasu kebabbun wuraren kasuwanci, da cibiyoyin tarihi da al’adu da yawon bude ido. An bayar da wannan kati a kalla 39,000 ga baki masu ziyara daga lokacin da aka kaddamar da shi a watan Yulin bara.

Haka nan, domin bai wa baki damar sanin tarihi da al’adun Sinawa a Beijing, a ranar 27 ga Disamban da ya gabata, birnin ya yi sabon albishir ta hanyar kaddamar da tsarin kai bakin da suka yada zango a cikinsa ziyara ta rabin yini a wasu muhimman wurare kyauta. Ana gudanar da wannan tsari sau biyu a yini, da safe da kuma maraice.

Sauran biranen kasar Sin kamar Shanghai su ma suna ci gaba da janyo hankulan dubban masu kawo ziyara saboda manufar shigowa ba tare da biza ba. A watannin baya-bayan nan, alal misali, ana samun karuwar maziyartan Koriya ta Kudu dake tururuwa zuwa birnin Shanghai. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Babu Wanda Zai Ci Nasara A Yakin Cinikayya Ko Yakin Harajin Kwastam

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.