• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Dakatar Da Duk Wani Tashin Hankali A Gabashin Kongo

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Dakatar Da Duk Wani Tashin Hankali A Gabashin Kongo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Jumma’a, babban jakadan kasar Sin na kujerar din-din-din a Majalisar Dinkin Duniya, Fu Cong ya bayyana cewa, har yanzu dai halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo (DRC) na ci gaba da tabarbarewa, kuma kasar Sin na fatan dukkan bangarorin da abin ya shafa su yi biyayya ga kiraye-kirayen da kasashen duniya da kwamitin sulhu na MDD ke yi musu, ta hanyar gaggauta dakatar da duk wani tashin hankali, da kuma kaurace wa duk wani mataki da ka iya ta’azzara zaman dar-dar.

A yayin da yake jawabi a kan kuri’ar daftarin kwamitin sulhun game da halin da ake ciki a kasar ta DRC, Jakadan ya ce rikicin da ya barke a baya-bayan nan a gabashin kasar ta DRC wanda aka dauki tsawon makwanni ana tafkawa, duk ya addabi kasashen duniya.

  • Akwai Babban Aiki A Gabana, Cewar Amorim
  • Yadda Ake Haɗa Kayan Ƙamshi Na Miya (Spices)

Fu ya kara da cewa, bayan kungiyar ’yan tawaye ta M23 ta kwace birnin Goma, wanda ya saba wa kiran da kasashen duniya da na shiyya-shiyya suka yi na tsagaita bude wuta, da kuma keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta na kashin kanta da ta yi, ta sake kame birnin Bukavu da sauran wurare, lamarin da ya kara rura wutar rikicin a gabashin DRC, tare da kara haifar da fargabar fantsamar rikicin zuwa na yanki baki daya.

Jakadan ya kuma ce, kudurin da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da shi ba da jimawa ba, ya bukaci kungiyar ta M23 da ta gaggauta tsagaita wuta tare da ficewa daga yankunan da ta mamaye. Wannan kuma ya yi dai-dai da fatan kasashen duniya da kasashen yankin na ganin an tsagaita bude wuta da kuma dakatar da rikicin, sannan kuma wani mataki ne da kwamitin sulhun ya dauka don sauke nauyin da ya rataya a wuyansa.

Mista Fu ya nanata cewa, kasar Sin na nuna goyon baya sosai ga warware matsalolin Afirka ta hanyar da ta dace da nahiyar, yana mai jaddada cewa, kamata ya yi a tsara kudurorin kwamitin sulhu na MDD da za su taimaka wa tafiyar da harkokin shiyya-shiyya, don samar da daidaito da kokarin sulhu a matakin shiyya-shiyya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Labarai Masu Nasaba

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Sha Domin Ƙarin Ni’ima Ga Mata

Next Post

Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

Related

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

19 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

19 hours ago
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

19 hours ago
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

20 hours ago
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

21 hours ago
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

22 hours ago
Next Post
Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.