ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

by Bello Hamza and Sulaiman
10 months ago
Dantsoho

Kungiyoyi da kuma sauran abokan arziki, ba ci gaba data taya Shugaban Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA Dakta Abubakar Dantsoho bisa zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Jiragen Ruwa ta duniya wato IAPH.

Daya daga cikin su ita ce, Hukumar Sufurin Jiragen Ruwa ta Kasa  wato NSC wadda Sakatarenta kuma shugabanta Dakta Akutah Pius Ukeyima, ya bayyana cewa, zabar Dantsoho a mukamin hakan ya nuna salon shugabancinsa, na tafiyar da Hukumar ta NPA, musamman yadda ya mayar da hankali, wajen kara bunkasa fannin na sufurin kasar.

“Wannan nasarar da  Dantsoho ya samu babban abin alfahari ne, ga kasar nan wanda kuma hakan ya nuna irin shugabanci na gari na Dantsoho ke ci gaba da yi ne, a bangaren Hukumar da kuma a bangren ruwa,” Inji Dakta Akutah.

ADVERTISEMENT

Kazalika, Hukumar ta kuma jinjinawa Dakta Dantsoho kan samar da dabarun tsare-tsaren da suka kara saita fannin sufuri a kasar da kuma a fadin duniya.

Ya bayyana kwarin guiwarsa da cewa, shugabancin na Dantsoho, ya taimaka matuka wajen samar da damarmaki da dama a nahiyar Afirka, wanda hakan ya kuma kai Nijeriya ga wani babban mataki a bangaren sufurin Jiragen Ruwa a Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

Ya kuma sanar da ci gaba da bai wa shugabancin Dakta Dantsoho goyon baya, musaman domin kara samar da sauye-sauyen da za su kara bunkasa hada-hadar zirga-zirga, da kuma a bangaren kara bunkasa kasuwancin tatalin azrki na Teku.

A nan kuma Kamfanin Rukunonin SIFAD, ya taya Dakta Dantsoho murnar zama Mataimakin Shugaban na kungiyar ta IAPH.

Hakan na kunshe ne, a cikin wata wasika da Shugaban Kamfanin Dakta Taiwo Afolabi CON ya fitar ta taya murnar, inda ya danganta zabar Dantsoho kan mukamanin a matsyin abinda ya dace, musamman duba irin salon shugabanci na gari na Dakta Dantsoho, wanda hakan ya sanya ya samar da gagarumar gudunmawa a bangaren sufurin Jiragen Ruwa na kasar.

Shugaban sashen samar da bayanai na Kamfanin  Mista Olumuyiwa Akande, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar.

“Wannan zaben na ka ya nuna irin kwarewar da kake da ita da kuma shekarun da ka shafe, kana yiwa Hukumar aiki wadda ta faro tun daga lokacin da ka yi aikin yiwa kasa hidima a Hukumar a shekarar 1992, inda a yanzu kuma ka kasance shugaban Hukumar ta NPA, “ A cewar Afolabi.

Ya kara da cewa, iya salon shugabanci na gari da kuma sauye-sayen da Dakta Dantsoho ya samar a hukumar, sun kara karfafa ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar.

A cewarsa, nasarorin da shugaban ya samar a Hukumar ba wai Hukumar ce kadai za ta amfana ba, har da daukacin fadin nahiyar Afirka

Kamfanin ya kuma bayyana kwarin airin Dakta Dantsoho zai yi amfani da sabbin dabarunsa na kara karfafa hadaka domin kai Afirka .

“Kamfanin na alfahari da nasarorin da ka samar da kuma ci gaba da kara ciyar da Hukumar gaba,”Inji Afolabi.

Kazalika, Kamfanin na SIFAD ya kuma kara jaddda goyon bayansa kan shiye-shiryen da Hukumar ke ci gaba da yin a kara ciyar da Hukumar gaba

Ya kuma ayyana ci gaba da yin hadaka da Hukumar ta NPA, musamman domin kara fadada gasa a bangaren sufurin Jiragen Ruwa na kasar.

Dantsoho
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya
Dantsoho
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Next Post
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

LABARAI MASU NASABA

Ta’addanci

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda Takwas A Katsina

July 9, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.