• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Sabuwar Cuta: Manoman Dankalin Turawa Sun Karaya

by Abubakar Abba
3 years ago
Dankalin Turawa

Wasu daga cikin manoman dankalin Turawa a jihar Filato sun bayyana farbagarsu ta cewa, bana za su samu gibi mai yawa, saboda bullar wata sabuwar cuta da ke yi wa dankalin illa.

Jihar Fitalto na daya daga cikin jihohin da ke kan gaba a kasar nan wajen noman dankalin Turawa tare da fitar da shi zuwa yankunan kasar nan domin sayarawa.

  • Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista
  • Hisbah Ta Jadadda Muhimmancin Gwajin Lafiya Kafin Aure 

Sun kuma koka kan yadda irin na dankalin ke yin matukar tsada daga watan Afirilu zuwa watan Mayu na kowace shekara, inda suka kara da cewa, hakan na shafar fara da dashensu na dankalin.

Sai dai, Sun danganta tashin farashin na irin kan yadda kayan masarufi ke kara yin tashin gwaron zabo a kasar nan.

Sun sanar da cewa, buhu daya na irin dankalin an sayar da shi a bara,a kan naira 15,000, amma a yanzu, ana sayar da shi kan naira 20,000 zuwa naira 22,000, inda wannan tsadar ta janyo wa wasu manomansa da dama, ba za su iya yin noman dankalin a bana ba.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Amma duk da wannan kalubalen, wasu manoman ba su fitar da ran samun amfaninsa mai yawa ba.

Wasu daga cikin manoman da cutar ta lalata musu amfaninsu sun bayyana cewa, hakan ya janwo musu yin asarar kudinsu da suka zuba wajen yin nomansa.

Daya daga cikin manoman, Uwargida Atong James ta ce, ta dasa irin dankalin buhu biyu a gonarta a bana.

Matar wadda gonarta take a yankin Lamingo a garin Jos, ta ce, ta haki kimanin kashi 70 daga cikin dari na dankalin, amma ko cikakken buhu daya ba ta iya samu ba.

Uwargida Atong ta ci gaba da cewa, idan ta dasa buhu biyu zuwa uku na irin dankalin Turawam tana samun daga buhu 12 zuwa 15, amma saboda bullar cutar, ta yi asara sosai. Idan ta dasa buhu biyu zuwa uku na irin dankalin Turawam tana samun daga buhu 12 zuwa 15, amma saboda bullar cutar, ta yi asara sosai a bana.

Ta kara da cewa, ta daina noman dankalin Turawan, inda a yanzu ta koma noman albasa da masara da rogo da kuma Kabeji.

Saboda irin wannan yanayin na yanzu kan noman dankalin na Turawa a yankin, za a ci gaba da samun karancin irin na dankalin Turawan.

Tabbas bisa ga irin wannan yanayin da manonsa ke fusknta na karancin irin zai yi wa karamin manominsa wahala matuka, musamman a yankin.

Ta bayyana cewa, domin a magance matsalar, akwai matukara bukatar mahukunta su kawo wa fannin dauki, musamman wajen samar da wadataccen irin na dankalin Turawa da kuma dakile yaduwar cutar.

Shi ma wani manomin na dankalin Turawa mai suna Bitrus Mador ya bayyana cewa, bullar cutar ba karamar barazana ba ce ga manoman na dankalin da ke yin noma a yankin.

Bitrus ya kara da cewa, an bayyana cewa, cutra ta bulla ne saboda samun canjin yanayi wanda hakan ya fi aukuwa a lokacin damina.

A cewarsa, wadanda suka dasa dankalin a watan Afirilu sun sa a cutar ba ta harbi dankalin da suka dasa sosai ba, inda ya kara da cewa, ya dasa buhu shida na irin na dankalin a cikin kimainin wata shida.

Shi ma wani manomin dankalin mai suna Mador ya sanar da cewa, tuni dankalin da ya dasa ya fara nuna alamar harbuwa da cutar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Next Post
Ma’aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

Ma'aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.