ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Sabuwar Cuta: Manoman Dankalin Turawa Sun Karaya

by Abubakar Abba
4 years ago
Dankalin Turawa

Wasu daga cikin manoman dankalin Turawa a jihar Filato sun bayyana farbagarsu ta cewa, bana za su samu gibi mai yawa, saboda bullar wata sabuwar cuta da ke yi wa dankalin illa.

Jihar Fitalto na daya daga cikin jihohin da ke kan gaba a kasar nan wajen noman dankalin Turawa tare da fitar da shi zuwa yankunan kasar nan domin sayarawa.

  • Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista
  • Hisbah Ta Jadadda Muhimmancin Gwajin Lafiya Kafin Aure 

Sun kuma koka kan yadda irin na dankalin ke yin matukar tsada daga watan Afirilu zuwa watan Mayu na kowace shekara, inda suka kara da cewa, hakan na shafar fara da dashensu na dankalin.

ADVERTISEMENT

Sai dai, Sun danganta tashin farashin na irin kan yadda kayan masarufi ke kara yin tashin gwaron zabo a kasar nan.

Sun sanar da cewa, buhu daya na irin dankalin an sayar da shi a bara,a kan naira 15,000, amma a yanzu, ana sayar da shi kan naira 20,000 zuwa naira 22,000, inda wannan tsadar ta janyo wa wasu manomansa da dama, ba za su iya yin noman dankalin a bana ba.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Amma duk da wannan kalubalen, wasu manoman ba su fitar da ran samun amfaninsa mai yawa ba.

Wasu daga cikin manoman da cutar ta lalata musu amfaninsu sun bayyana cewa, hakan ya janwo musu yin asarar kudinsu da suka zuba wajen yin nomansa.

Daya daga cikin manoman, Uwargida Atong James ta ce, ta dasa irin dankalin buhu biyu a gonarta a bana.

Matar wadda gonarta take a yankin Lamingo a garin Jos, ta ce, ta haki kimanin kashi 70 daga cikin dari na dankalin, amma ko cikakken buhu daya ba ta iya samu ba.

Uwargida Atong ta ci gaba da cewa, idan ta dasa buhu biyu zuwa uku na irin dankalin Turawam tana samun daga buhu 12 zuwa 15, amma saboda bullar cutar, ta yi asara sosai. Idan ta dasa buhu biyu zuwa uku na irin dankalin Turawam tana samun daga buhu 12 zuwa 15, amma saboda bullar cutar, ta yi asara sosai a bana.

Ta kara da cewa, ta daina noman dankalin Turawan, inda a yanzu ta koma noman albasa da masara da rogo da kuma Kabeji.

Saboda irin wannan yanayin na yanzu kan noman dankalin na Turawa a yankin, za a ci gaba da samun karancin irin na dankalin Turawan.

Tabbas bisa ga irin wannan yanayin da manonsa ke fusknta na karancin irin zai yi wa karamin manominsa wahala matuka, musamman a yankin.

Ta bayyana cewa, domin a magance matsalar, akwai matukara bukatar mahukunta su kawo wa fannin dauki, musamman wajen samar da wadataccen irin na dankalin Turawa da kuma dakile yaduwar cutar.

Shi ma wani manomin na dankalin Turawa mai suna Bitrus Mador ya bayyana cewa, bullar cutar ba karamar barazana ba ce ga manoman na dankalin da ke yin noma a yankin.

Bitrus ya kara da cewa, an bayyana cewa, cutra ta bulla ne saboda samun canjin yanayi wanda hakan ya fi aukuwa a lokacin damina.

A cewarsa, wadanda suka dasa dankalin a watan Afirilu sun sa a cutar ba ta harbi dankalin da suka dasa sosai ba, inda ya kara da cewa, ya dasa buhu shida na irin na dankalin a cikin kimainin wata shida.

Shi ma wani manomin dankalin mai suna Mador ya sanar da cewa, tuni dankalin da ya dasa ya fara nuna alamar harbuwa da cutar.

Dankalin Turawa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Ma’aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

Ma'aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.