ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Sabuwar Cuta: Manoman Dankalin Turawa Sun Karaya

by Abubakar Abba
4 years ago
Dankalin Turawa

Wasu daga cikin manoman dankalin Turawa a jihar Filato sun bayyana farbagarsu ta cewa, bana za su samu gibi mai yawa, saboda bullar wata sabuwar cuta da ke yi wa dankalin illa.

Jihar Fitalto na daya daga cikin jihohin da ke kan gaba a kasar nan wajen noman dankalin Turawa tare da fitar da shi zuwa yankunan kasar nan domin sayarawa.

  • Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista
  • Hisbah Ta Jadadda Muhimmancin Gwajin Lafiya Kafin Aure 

Sun kuma koka kan yadda irin na dankalin ke yin matukar tsada daga watan Afirilu zuwa watan Mayu na kowace shekara, inda suka kara da cewa, hakan na shafar fara da dashensu na dankalin.

ADVERTISEMENT

Sai dai, Sun danganta tashin farashin na irin kan yadda kayan masarufi ke kara yin tashin gwaron zabo a kasar nan.

Sun sanar da cewa, buhu daya na irin dankalin an sayar da shi a bara,a kan naira 15,000, amma a yanzu, ana sayar da shi kan naira 20,000 zuwa naira 22,000, inda wannan tsadar ta janyo wa wasu manomansa da dama, ba za su iya yin noman dankalin a bana ba.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Amma duk da wannan kalubalen, wasu manoman ba su fitar da ran samun amfaninsa mai yawa ba.

Wasu daga cikin manoman da cutar ta lalata musu amfaninsu sun bayyana cewa, hakan ya janwo musu yin asarar kudinsu da suka zuba wajen yin nomansa.

Daya daga cikin manoman, Uwargida Atong James ta ce, ta dasa irin dankalin buhu biyu a gonarta a bana.

Matar wadda gonarta take a yankin Lamingo a garin Jos, ta ce, ta haki kimanin kashi 70 daga cikin dari na dankalin, amma ko cikakken buhu daya ba ta iya samu ba.

Uwargida Atong ta ci gaba da cewa, idan ta dasa buhu biyu zuwa uku na irin dankalin Turawam tana samun daga buhu 12 zuwa 15, amma saboda bullar cutar, ta yi asara sosai. Idan ta dasa buhu biyu zuwa uku na irin dankalin Turawam tana samun daga buhu 12 zuwa 15, amma saboda bullar cutar, ta yi asara sosai a bana.

Ta kara da cewa, ta daina noman dankalin Turawan, inda a yanzu ta koma noman albasa da masara da rogo da kuma Kabeji.

Saboda irin wannan yanayin na yanzu kan noman dankalin na Turawa a yankin, za a ci gaba da samun karancin irin na dankalin Turawan.

Tabbas bisa ga irin wannan yanayin da manonsa ke fusknta na karancin irin zai yi wa karamin manominsa wahala matuka, musamman a yankin.

Ta bayyana cewa, domin a magance matsalar, akwai matukara bukatar mahukunta su kawo wa fannin dauki, musamman wajen samar da wadataccen irin na dankalin Turawa da kuma dakile yaduwar cutar.

Shi ma wani manomin na dankalin Turawa mai suna Bitrus Mador ya bayyana cewa, bullar cutar ba karamar barazana ba ce ga manoman na dankalin da ke yin noma a yankin.

Bitrus ya kara da cewa, an bayyana cewa, cutra ta bulla ne saboda samun canjin yanayi wanda hakan ya fi aukuwa a lokacin damina.

A cewarsa, wadanda suka dasa dankalin a watan Afirilu sun sa a cutar ba ta harbi dankalin da suka dasa sosai ba, inda ya kara da cewa, ya dasa buhu shida na irin na dankalin a cikin kimainin wata shida.

Shi ma wani manomin dankalin mai suna Mador ya sanar da cewa, tuni dankalin da ya dasa ya fara nuna alamar harbuwa da cutar.

Dankalin Turawa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Ma’aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

Ma'aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

LABARAI MASU NASABA

Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.