ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bullar Sabuwar Cuta: Manoman Dankalin Turawa Sun Karaya

by Abubakar Abba
4 years ago
Dankalin Turawa

Wasu daga cikin manoman dankalin Turawa a jihar Filato sun bayyana farbagarsu ta cewa, bana za su samu gibi mai yawa, saboda bullar wata sabuwar cuta da ke yi wa dankalin illa.

Jihar Fitalto na daya daga cikin jihohin da ke kan gaba a kasar nan wajen noman dankalin Turawa tare da fitar da shi zuwa yankunan kasar nan domin sayarawa.

  • Ko Makiyan Buhari Sun San Aikin Da Ya Yi Yafi Na Gwamnatocin Baya -Minista
  • Hisbah Ta Jadadda Muhimmancin Gwajin Lafiya Kafin Aure 

Sun kuma koka kan yadda irin na dankalin ke yin matukar tsada daga watan Afirilu zuwa watan Mayu na kowace shekara, inda suka kara da cewa, hakan na shafar fara da dashensu na dankalin.

ADVERTISEMENT

Sai dai, Sun danganta tashin farashin na irin kan yadda kayan masarufi ke kara yin tashin gwaron zabo a kasar nan.

Sun sanar da cewa, buhu daya na irin dankalin an sayar da shi a bara,a kan naira 15,000, amma a yanzu, ana sayar da shi kan naira 20,000 zuwa naira 22,000, inda wannan tsadar ta janyo wa wasu manomansa da dama, ba za su iya yin noman dankalin a bana ba.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Amma duk da wannan kalubalen, wasu manoman ba su fitar da ran samun amfaninsa mai yawa ba.

Wasu daga cikin manoman da cutar ta lalata musu amfaninsu sun bayyana cewa, hakan ya janwo musu yin asarar kudinsu da suka zuba wajen yin nomansa.

Daya daga cikin manoman, Uwargida Atong James ta ce, ta dasa irin dankalin buhu biyu a gonarta a bana.

Matar wadda gonarta take a yankin Lamingo a garin Jos, ta ce, ta haki kimanin kashi 70 daga cikin dari na dankalin, amma ko cikakken buhu daya ba ta iya samu ba.

Uwargida Atong ta ci gaba da cewa, idan ta dasa buhu biyu zuwa uku na irin dankalin Turawam tana samun daga buhu 12 zuwa 15, amma saboda bullar cutar, ta yi asara sosai. Idan ta dasa buhu biyu zuwa uku na irin dankalin Turawam tana samun daga buhu 12 zuwa 15, amma saboda bullar cutar, ta yi asara sosai a bana.

Ta kara da cewa, ta daina noman dankalin Turawan, inda a yanzu ta koma noman albasa da masara da rogo da kuma Kabeji.

Saboda irin wannan yanayin na yanzu kan noman dankalin na Turawa a yankin, za a ci gaba da samun karancin irin na dankalin Turawan.

Tabbas bisa ga irin wannan yanayin da manonsa ke fusknta na karancin irin zai yi wa karamin manominsa wahala matuka, musamman a yankin.

Ta bayyana cewa, domin a magance matsalar, akwai matukara bukatar mahukunta su kawo wa fannin dauki, musamman wajen samar da wadataccen irin na dankalin Turawa da kuma dakile yaduwar cutar.

Shi ma wani manomin na dankalin Turawa mai suna Bitrus Mador ya bayyana cewa, bullar cutar ba karamar barazana ba ce ga manoman na dankalin da ke yin noma a yankin.

Bitrus ya kara da cewa, an bayyana cewa, cutra ta bulla ne saboda samun canjin yanayi wanda hakan ya fi aukuwa a lokacin damina.

A cewarsa, wadanda suka dasa dankalin a watan Afirilu sun sa a cutar ba ta harbi dankalin da suka dasa sosai ba, inda ya kara da cewa, ya dasa buhu shida na irin na dankalin a cikin kimainin wata shida.

Shi ma wani manomin dankalin mai suna Mador ya sanar da cewa, tuni dankalin da ya dasa ya fara nuna alamar harbuwa da cutar.

Dankalin Turawa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Ma’aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

Ma'aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.