• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila?

by Abba Ibrahim Wada
4 months ago
in Wasanni
0
Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yadda wasanni suke tafiya tabbas kungiyar kwallon kafa ta Liberpool ta kama hanyar lashe gasar Premier na bana in dai ba wani gagarumin sammatsi ba – bayan da ta kara kankane matsayinta na daya a tebur da tazarar maki 13, wanda hakan ya nuna kungiyar ta nufi hanyar lashe kofin da aka yi zaton Manchester City ko Arsenal daya a cikinsu ne zai lashe a kakar ta bana.

Idan muka duba tarihi babu wata kungiya a tarihin babbar gasar ta Ingila, tun daga kakar wasa ta 1888 zuwa 1889, da ta taba yin wannan fintinkau a wannan mataki na gasar kuma a ce ba ta dauki kofin ba kuma a halin yanzu ma Liberpool din tana kan ganiyarta na lashe wasa ga duk kungiyar da ta hadu da ita a hanya. Tsohon dan wasan Ingila, Gary Lineker ma cewa ya yi, “Abin ya fara tashi daga gasa ya zama tamkar.

  • Fa’ida Daga Tafsirin AlÆ™ur’ani Na Ibnu Juzai [1]
  • Shawarwari Kan Kayyade Amfani Da Siga

tattaki ko ba haka ba ne?” Duk tsawon wannan kakar Liberpool ta yi rashin nasara ne sau daya kawai a gasar ta Premier.

Mai bi mata a baya-a baya, kungiyar Arsenal ta zubar da maki a dukkanin wasanninta biyu na baya-bayan nan ciki har da wanda ta yi canjaras ba ci da Nottingham Forest da kuma rashin nasara a hannun kungiyar kwallon kafa ta West Ham United har gida. Amma kociyan kungiyar ta Liberpool Arne Slot ya ce: “Har yanzu da sauran tafiya, wasa 10 ba nan ba ne…

Ya ce “Yanzu ‘yanwasan suna da hutu, daga nan za mu mayar da hankali kan wasanmu na Zakarun Turai da Paris St-Germain fiye da yadda muka mayar da hankali a kan teburin Premier,” in ji kociyan. Amma Ko kociyan Arsenal Mikel Arteta, yanzu dole ya san cewa kusan kasuwa ta riga ta ci ta cinye – ta tashi – to amma kafin wasansu da Forest ya ce shi bai sallama ba – bakin rai bakin fama.

Labarai Masu Nasaba

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don ÆŠaukar Mbeumo Daga Brentford

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

Bayan wasan na Forest, Mikel Arteta ya gaya wa manema labarai cewa – haka abin yake ba bambanci mako daya baya, da mako biyu baya, da ma wata uku baya. Ya ce abin kawai da za su yi yanzu shi ne su tabbatar suna cin wasanninsu su ga maki nawa za su samu – kenan dai har yanzu, Artetan bai sallama ba – yana ganin cinta duk da tazarar da ke tsakaninsu da Liberpool din.

To amma tsohon danwasan gaba da gefe na Liberpool Stebe McManaman, ya ce ai babu wata tantama ba wata tababa Liberpool a wannan kadami tamkar wani ingarman doki ne da ya kama hanyar cin gasa ba mai shiga gabansa sai dai a hangi kurarsa kuma duk sauran kungiyoyin sai zubewa suke suna taimaka wa Liberpool din.

Kungiyar kwallon kafa ta Nottingham Forest na ta uku a tebur da bambancin maki shida a bayan Arsenal, ita ma kuma Manchester City – wadda sau hudu tana cin kofin na Premier a jere – na bayan Forest din da maki daya wanda hakan ya nuna irin bajintar da kungiyar Forest ta nuna karkashin kociyanta dan Portugal, Nuno Espirito Santos, wanda a baya ya taba koyar da Wolbes.

A tarihi kungiya daya ce kawai ta taba wannan fintinkau da maki 13, kuma ba ta dauki kofin na Premier ba – lokacin da kiri-da-muzu Manchester United na ji tana gani kuma Arsenal ta yi gaba da kofin a kakar 1997-98 – to amma wannan tun a farkon kakar ne Utd din ta bayar da tazarar da ta zama tamkar sammakon-bubukuwa.

Wanne Lokaci Liberpool Za Ta Zama Zakara?

Ba zai zama riga-mallam-masallaci ba a ce kungiyar Liberpool ta zama zakarun Premier masu jiran-gado a yanzu – magana ce kawai ta yaushe amma ba idan har ba domin kamfanin kididdiga kan harkokin wasanni na Birtaniya- Opta- ya ce akwai yuwuwa kashi 98.7 cikin dari Liberpool ce za ta dauki kofin na Premier, yayin da Arsenal ke da dama ta kashi 1.3 cikin dari.

Liberpool ta yi wa Arsenal fintinkau da tazarar maki 13, yayin da ya rage wasa 10 a kammala gasa – koda yake Arsenal na da ragowar 11, sannan idan har Liberpool ta ci gaba da wannan tazara ta maki 13, wannan zai sa ta ci kofin da ragowar wasa hudu a nade tabarmar gasar – ranar 26 ga watan Afirilu kenan a wasanta da kungiyar kwallon kafa ta Tottenham.

To amma idan Arsenal ta ci kwantan wasanta daya ta kuma yi daidai da sauran sakamakonta to Liberpool, za ta dauki kofin a karshen mako mai zuwa a wasanta da Chelsea. Idan har haka ta tabbata wasansu na farko a matsayin zakarun Premier zai kasance a gida da Arsenal, wadda za ta iya musu rakiyar shiga fili a matsayin zakaru, wanda a tarihi haka ake yi.

Saboda ci gaban da suke samu a gasar Zakarun Turai da kuma matsayinsu a gasar kofin Carabao na wasan karshe da Newcastle da kuma hutun da za a iya na wasannin kasashe, Liberpool za ta yi wasa daye ne kawai na Premier a watan Maris kuma lokaci mafi kusa da Liberpool za ta iya daukar kofin na Premier a kididdiga shi ne makon farko na Afirilu.

Idan Liberpool din ta ci wasanninta uku na gaba kuma aka doke Arsenal a wasanninta hudu na gaba kuma kungiyoyin da ke bayansu suma suka zubar da maki ‘yan kalilan, to Liberpool za su zare kofin ranar


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FirimiyaIngilaLiverpool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da A Ce Ni Ba Dan Fim Ba Ne, Da Na Zama Malamin Addinin Musulunci -Baba Rabe

Next Post

Dalilin Da Ya Sa Aka Soke Wasan Barcelona Da Osasuna

Related

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don ÆŠaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don ÆŠaukar Mbeumo Daga Brentford

1 day ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

3 days ago
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 
Wasanni

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

3 days ago
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta BaÉ—i
Wasanni

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta BaÉ—i

3 days ago
Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika
Wasanni

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

4 days ago
Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6
Wasanni

Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6

5 days ago
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Aka Soke Wasan Barcelona Da Osasuna

Dalilin Da Ya Sa Aka Soke Wasan Barcelona Da Osasuna

LABARAI MASU NASABA

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan ÆŠaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe ÆŠan Kasuwa da ÆŠan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.