ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Sin

Bisa dalilai na zahiri, da matakai daban daban da mahukuntan kasar Sin ke aiwatarwa na zamanintar da kasa, muna iya cewa baya ga ci gaban da Sin ta cimma a wannan fage, su ma kawayenta, kuma abokan tafiya na kasashe masu tasowa musamman nahiyar Afirka, na iya koyon manyan darussa daga salon zamanintarwa na kasar. Cikin ginshikan cimma nasara da ake lura da su a wannan fage akwai batun yaki da fatara, da gina ababen more rayuwa, da bunkasar sashen kirkire-kirkiren fasahohi wadanda ka iya zamewa kasashen nahiyar Afirka kyawawan darussa a kan turbarsu ta bunkasa kai.

 

Alal hakika, kasar Sin ta yi aiki tukuru, inda ta tashi daga matsayin babbar kasar manoma zuwa cibiyar kere-kere da hada-hadar tattalin arziki ta duniya. Gwamnatin Sin ta yi aiki tukuru wajen tsame miliyoyin ’yan kasar daga kangin fatara, tare da himmatuwa wajen rage gibin dake akwai tsakanin mawadata da talakawa, da ma birane da yankunan karkara. Wannan na nuni ga muhimmancin daidaita tafiya tsakanin bukatun raya tattalin arzikin al’umma da na bunkasa zamantakewarsu.

ADVERTISEMENT

 

Ko shakka babu kasashen Afirka ma na da matukar bukatar raya fannonin zamanintar da kai, musamman fannonin raya noma, da ayyukan gina layin dogo da hanyoyin mota, ta yadda hakan zai bayar da damar samarwa, da sarrafawa da safarar hajoji, da hidimomi, da zirga-zirga tsakanin al’ummu. Kana yayin da ake kokarin cimma wadannan burika, akwai babban misali da kasar Sin ta samar a wannan fage, wato samar da ci gaba ba tare da gurbata yanayi ko muhalli ba. A nan ya zama wajibi, yayin da kasashen Afirka ke kokarin samun ci gaba, su kuma kiyaye muhimmancin yaki da sauyin yanayi, da samar da isasshen makamashi mai tsafa, kamar dai yadda Sin ta wuce gaba wajen cin gajiyar makamashi mai tsafta da wanda ake iya sabuntawa, irin wadanda ake samarwa ta hasken rana da iska da sauransu, wadanda suka yi matukar dacewa da yanayin bukatu da albarkatun akasarin kasashen nahiyar ta Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

 

Tabbas fannonin zamanintar da kai na Sin na iya zama babbar taswira da kasashen Afirka ka iya bi, wajen kaiwa ga bunkasa yankuna, da kyautata zamantakewar al’ummunsu, da samar da isassun damammaki na gudanar da kyakkyawar rayuwa mai cike da walwala ga al’ummun nahiyar.(Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
  • Sulaiman
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

MASU ALAKA

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Next Post
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.