ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
11 months ago
Taki

Gidauniyar Wunti Al-Khair ta ƙaddamar da rabon takin zamani buhu 6,000 kyauta ga manoma a faɗin jihar Bauchi domin bunƙasa harkokin noma da wadata jihar da kayan abinci. 

 

Da ya ke jawabi a wajen ƙaddamar da rabon a ranar Alhamis, Abubakar Mohammed ‘Yanmaza, jami’in sa ido na gidauniyar, ya ce wannan rabon shi ne karo na huɗu da gidauniyar ke raba wa manoma kyautar takin zamani domin agaza musu a fannin noma.

ADVERTISEMENT
  • An Samu Gagarumin Ci Gaba Kan Habaka Fasahar Zamani Ta Sin Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Mai Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wani Yaro Ɗan shekara 2 A Yobe

Ya ce rabon na cikin manufar gidauniyar na taimaka wa manoma ne musamman masu ƙaramin karfi domin bunkasa harkokin noma a jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

“Kowa ya sani wadatar abinci yana ɗaya daga cikin alamun da ke nuna kyautatawar tattalin arziki na ƙasa baki ɗaya, don haka ne muka himmatu wajen ba da namu gudunmawar ta wannan fannin.”

 

Ya kara da cewa, an kafa gidauniyar ne domin taimakawa a ɓangaren kiwon lafiya, ilimi, tattalin arziki wanda rabon takin na daga cikin shirin gidauniyar na bunƙasa tattalin arziki, da kuma kyautata ci gaban al’umma.

 

“Wannan shi ne karo na huɗu da wannan gidauniyar ta ke rabon taki duk shekara ga manoma masu ƙaramin ƙarfi da ba za su iya sayen takin a irin wannan lokacin da gona ke buƙata ba.”

 

“An ware buhun taki guda 6,000 da za a rabar wa manoma masu ƙaramin karfi a dukkanin faɗin jihar Bauchi,” in ji shi.

 

‘Yanmaza ya nuna cewa an yi tsari na musamman domin tabbatar da asalin waɗanda aka zaɓo ne za su amfana da takin, ya yi gargaɗi kan cewa duk wanda aka kama da kauce wa asalin tsarin da aka samar da takin domin su zai ɗanɗana kuɗarsa.

 

Shi ma da ya ke ƙarin haske, jami’i a gidauniyar, Isyaka Isma’i Wunti, ya ce bayan ƙaddamar da rabon a cikin garin Bauchi za a zaga sauran shiyyoyin Bauchi da sauran yankuna domin yin rabon domin tabbatar da takin ya shigo hannun manoma a lungu da sako a na jihar.

 

Ya yi gargaɗin cewa kada waɗanda aka raba musu takin su je su sayar, ya nemi su tabbatar sun yi amfani da su ta hanyoyin da suka dace domin bunƙasa harkokin abinci da wata jihar da kayan abinci.

 

Ya kuma ce an yi adalci sosai wajen zaɓo masu cin gajiyar shirin a kowani lungu da sako. Inda ya ce an yi tsarin sosai na yadda asalin manoma kuma masu ƙaramin karfi ne za su amfana da tallafin.

 

Emmanuel Samson, daga cikin masu cin gajiyar tallafin, ya gode wa wanda ya assasa gidauniyar, Alhaji Bala Maija’ama Wunti bisa wannan tallafin, ya ce tallafin zai taimaka musu matuƙa wajen amfanin gona.

 

Salisu Muhammad Maidawa, ya ce, “Ba abin da za mu ce sai godiya ga wanda ya assasa wannan gidauniyar, yadda yake faranta wa jama’a rai ta fuskokin rayuwa daban-daban muna roƙon Allah ya faranta masa rai, abun da ya ke nema na alkairi Allah ya cika masa.”

 

“A zahirin gaskiya wannan tallafin ya zo a kan gaɓa domin kamar muna tsananin halin buƙatar takin zamani sai kuma ga shi Allah ya sa zan samu kyautarsa.”

 

Da yawan waɗanda suka ci gajiyar sun sha alwashin amfani da takin ta hanyoyin da su dace ba tare da sayarwa ba.

Taki
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Taki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa
  • Sulaiman
    An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara
  • Sulaiman
    2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
Labarai

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’
Labarai

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Next Post
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.