ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da A Ce Ni Ba Dan Fim Ba Ne, Da Na Zama Malamin Addinin Musulunci -Baba Rabe

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Fim

Jarumin Kannywood Abubakar Waziri ko kuma Baba Rabe kamar yadda wasu ke kiranshi ya bayyana batutuwa da dama da su ka shafi jaruman fim, yadda suke gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum da kuma yadda mutane ke kallonsu, Baba Rabe a wata hira da ya yi da DW ya ce akwai bukatar malamai su shigo cikin harkar Kannywood ka’in da na’in domin yanzu wani lokaci ne da mutane sunfi mayar da hankalinsu wajen kallon fina-finai fiye da wa’azozin malaman musulunci.

Abubakar Waziri wanda ya ce shi haifaffen birnin Zaria ne a Jihar Kaduna, ya yi karatu a makarantu da dama har ma da Jami’ar Ahmadu Bello inda ya samu shaidar kammala karatun Diploma a bangaren Al’adun gargajiya, bayan harkar fim ni ma’aikacin gwamnati ne inda nike aiki da ‘Abuja Council For Art And Culture’, amma tunda farko na fara aiki a Jami’ar Ahmadu Bello a matsayin dan wasan kwaikwayo a sashen Al’adun Gargajiya na makarantar inji shi.

  • Nijeriya Za Ta Nuna Gyare-gyaren Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu A Taron Kasuwanci A Faransa
  • Taro Na Uku Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin Ya Yi Zama Na Biyu

Ya kara da cewar kafin shiga masana’antar Kannywood na yi tafiye tafiye da dama wajen wakiltar Nijeriya a kasashe daban-daban da su ka hada da Amurka, China, Afrika Ta Kudu, Korea Ta Arewa, Korea Ta Kudu da sauran kasashen waje duk dai a fannin raye raye da wasan kwaikwayo, kuma cikin ikon Allah yanzu kuma gani a masana’antar Kannywood a matsayin jarumi.

ADVERTISEMENT

Da yake amsa tambaya a kan yadda wasu ke daukar jaruman masana’antar Kannywood a matsayin wasu mutane masu girman kai, Abubakar Waziri ya ce ko kusa wannan magana ba gaskiya bace, misali mu jaruman fim da muka kasance abinda bature ke kira ‘public figure’, muma muna da abubuwan da muke son aiwatarwa a rayuwar yau da kullum, idan na fito daga gida idan ba na yi fuska na yi tafiya ta ba, mutane da dama kan zo wajena domin daukar hotuna ko kuma yi mani tambayoyi a kan wasu fina-finai da na yi.

Idan hakan ta faru wani lokacin mutum ba zai samu damar da zai aiwatar da abin da ya fito gida domin ya aiwatar ba, don haka kamata yayi mutane su fahimce mu a maimakon su koma gefe su na kiranmu da masu ji da kai, Waziri ya ci gaba da cewar wannan dalili ne ya sa mutane ke yi masu kudin goro a duk lokacin da wani daga cikinsu ya aikata abinda ba daidai ba a maimakon a dora ma wanda ya yi laifin shi kadai sai ace ai duka yan fim haka suke.

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Daga karshe Abubakar Waziri Bado ya yi kira da a maimakon malamai su koma gefe su na zagi yan fim kamata ya yi ace su shigo cikin harkar a dama dasu, domin kuwa yanzu wani lokaci ne da ake ciki inda da dama mutane sun fi kallon fina-finai fiye da yadda su ke kallon karatuttukan malaman addini, saboda haka su shigo a hada karfi da karfe wajen kara tsaftace wannan masana’antar don kuwa ni ma kaina da ace ba jarumin fim bane ni , to da tabbas zan zama malamin addinin musulunci saboda ina matukar sha’awar ganin al’umma ta gyaru.

Fim
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila?

Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila?

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.