• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Fitar Da Sakamakon Bincike Game Da Yadda Kanada Ke Nuna Wa Kayayyakinta Wariya

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Bayan da ta shafe tsawon rabin shekara tana gudanar da bincike da tattaro shaidu, a jiya Jumma’a kasar Sin ta fitar da sakamakon binciken da ta yi, game da yadda kasar Kanada take nuna wa kayayyakinta wariya, sakamakon da ya nuna cewa, irin matakin da Kanada ta dauka a shekarar da ta gabata, wato kara sanya harajin kwastam kan wasu hajojin da ta shigar daga kasar Sin, ciki har da motoci masu aiki da lantarki, da karafa da kuma sanholo, salo ne na nuna wariya. Don haka, kasar Sin ta mayar da martani bisa doka, inda ta kara sanya harajin kwastam kan wasu hajojin Kanada, al’amarin da ya sa aka fitar da rahoton bincike kan kin yarda da salon wariya, wanda ya zama irinsa na farko a duk fadin duniya.

A watan Agustan shekarar da ta gabata ne, kasar Kanada ta sanar da kara sanya harajin kwastam da kaso dari bisa dari, kan motoci masu aiki da karfin lantarki kirar kasar Sin, wanda ya fara aiki daga watan Oktoban shekara ta 2024, tare da kara harajin kwastam na kaso 25 bisa dari kan hajojin karafa da sanholo da kasar Sin ta samar. Makasudin yin hakan shi ne, hada baki da kasar Amurka, wajen sanyawa motoci masu aiki da karfin lantarki da kayan karafa da sanholo kirar kasar Sin harajin kwastam. Manazarta sun yi nuni da cewa, hajojin kasar Sin ne kadai, ita Kanada ta kara wa harajin kwastam, kuma ba tare da gudanar da cikakken bincike ba. Kana, fitar da irin wannan sanarwa ba tare da wata ingantacciyar hujja ba, salon wariya ne da Kanada ta yi, wanda ya kawo illa ga tsarin cinikayya na kasa da kasa.

  • A Mai Da Duniya Ta Zama Ta Kasa Da Kasa
  • Manchester United Na Son Lashe Firimiya A Shekarar 2028

Rahotannin sun kuma ruwaito cewa, a matsayinta na gani-kashe-nin Amurka, gwamnatin kasar Kanada ta sha nuna adawa da kasar Sin. Amma ba ta samu abun da take so ba. Tun bayan da sabuwar gwamnatin Amurka ta fara aiki tsawon kwanaki 40 ko fiye, ya zuwa yanzu, sau da dama ta ci zarafin Kanada, inda ta ce Kanada “jiha ce ta 51 a Amurka”, har ma ta yi mata barazana ta hanyar sanya harajin kwastam. Irin wannan abun ya zama gargadi ga wasu kasashe ’yan kalilan, wadanda ke fatan samun “afuwa” daga Amurka, bisa matakin da suka dauka kan kasar Sin.

Kasar Sin ba za ta rura wutar rikici ba, amma ba ta tsoro. Kuma tabbas za ta tsaya ga kiyaye muradun kasa da ikon samar da ci gaba, da kiyaye ka’idojin WTO game da tsarin cudanyar sassan kasa da kasa a fannin kasuwanci. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.